• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dauki Darasi A Zaben 2023 – Shugaban INEC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Mahmood Yakubu ya bayyana cewa sun yi matukar daukar darasi a zaben 2023, sannan za su kara kwazo a zaben gwamnoni da zai gudanar a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.

Ya kara da cewa hukumar ta gamsu da irin martanin da ta samu a yayin bitar bayan zaben 2023 da hukumar ta shirya.

  • NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri
  • Yadda Amurka Ke Kwaton Albarkatun Kasa Da Kasa Da Sunan Yaki Da Ta’addanci

Shugaban INEC ya bayyana hakan ne a jim kadan bayan kammala bitar zaben 2023 na kwanaki uku da ya gudana a Jihar Legas, inda ya tabbatar da cewa za a magance matsalolin da suka faru a lokacin zaben da tare da yin amfani da shawarwarin da hukumar ta samu domin inganta zaben kasar nan, wanda hukumar za ta fara yin gwaji a zabukan gwamnoni da za su gudana a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.

“Mun yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin cewa za mu gudanar da bitar zaben 2023 a cikin wata daya. Mun fara ne tun daga ranar 4 ga watan Yulin har zuwa 4 ga watan Agusta, mun samu korafe-korafe mai matukar yawan gaske. Mun fara gudanar da taron tattaunawa na shawarwari da kwamishinoninmu da ke jihohi, sannan muka zarce har zuwa wurin kungiyoyin sufuri, kafin muka shigo da jam’iyyu da sauran kungiyoyin fararen huda da dai sauransu. Gaba daya dai, muna samun kwarin gwiwa ta hanyar martanin masu ruwa da tsaki a fadin hukumar da irin gudunmawar da suka bayarwa.

“Mun samu matsaloli masu yawa tu daga wurin tantance masu kada kuri’a har zuwa saka sakamakon zabe a na’ura, sai dai mun samu shawarwari a kan haka.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

“Akwai batun kalubalen kai kayayyakin zabe da yadda za a fara zabuka a kan lokaci da da samar da katin zabe da kuma amsa katin da sauransu. Muna samu korafe-korafe masu yawa kuma mun samu shawarwari a kan lamarin, inda wadanda hukumar za ta iya magancesu a ofis, za ta yi hakan, wadanda kuma ke bukatar gyara ga dokokin zabe ne ko kundin tsarin mulki za mu kai su zauren majalisar kasa domin duba lamarin. Don haka mun yi farin ciki da martanin da muka samu da kuma tattaunawa da muka yi a hukumar. Abu mafi muhimmanci ga hukumar shi ne, mun ji ta bakin ‘yan Nijeriya kuma hakan zai ba mu damar komawa kan turbar hukumar domin ci gaba da inganta zaben kasar nan.

“Bayan mun samu wadannan korafe-korafe, hakan zai ba mu damar yin gyare-gyare a zabukan gwamnoni da za su gudana a jihohin Bayelsa, Imo da kuma Kogi a watan Nuwamba, domin za mu kaddamar da wasu daga cikin shawarwarin da muka samu wadanda suka kunshi hukumar, amma wadanda suka kunshi majalisa, majalisar kasa za ta yi aiki ne bisa tanadin dokokin kasar nan.

“Haka kuma akwai wata damar da muka da ita, saboda a halin yanzu kwai zaben cike gurbi har guda hudu da suka hada da mazaba Surulere 1 a Jihar Legas da mazabar Jalingo da ke Jihar Taraba da mazabar Chibok da ke Jihar Borno State da kuma mazabar Chikun da ke Jihar Kaduna. Za mu ci gaba da kaddamar da wasu shawarwarin a zabukan cike gurbi da ke tafe.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ofishin Jakadancin Sin A Ghana Ya Bude Cibiyar Bayar Da Visa

Next Post

El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.