• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dukufa Magance Matsalolin Bangaren Lantarki, In Ji Minista

by Khalid Idris Doya
2 years ago
lantarki

Gwamnatin tarayya ta ce ta dukufa wajen ganin ta shawo kan asalin matsalolin da suke addabar bangaren wutar lantarki tare da nemo mafita a kansu.

Ministan wutan lantarki, Adebayo Adelabu shi ne ya shaida hakan a lokacin da ke ganawa da ‘yan jarida jim kadan bayan ganawa da ya yi da wasu masu ruwa da tsakani na jam’iyyar APC a sakateriyar jam’iyyar na Jihar Oyo da ke Oke-Ado a Ibadan.

  • Abubuwa 10 Da Ya Kamata A Sani Game Da Sabon Tsarin Biyan Kudin Wutar Lantarki
  • Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Ministan ya ce Shugaban kasa, Bola Tinubu ya himmatu wajen kawo gagarumin sauyi a bangaren wutar lantarki.

Ya ce, “Bari na yi amfani da wannan damar na tabbatar wa al’ummar Nijeriya cewa gwamnatin Bola Tinubu a shirye take wajen ganin ta sauya abubuwan da suke faruwa a harkar wutar lantarki, ta canja takun da ke bangaren. Wannan dalilin ne ya sa yanzu muka dukufa wajen shawo kan asalin matsalolin wutar lantarki.

“Muna yin wannan aikin shawo kan dukkanin matsalolin ne tare da yin aikin hadin guiwa da dukkanin masu ruwa da tsaki a bangaren domin nemo mafita, kama daga bangaren samar da gas zuwa tarawa, watsawa da kuma rarraba wutar lantarki hadi da su kansu kwastomomi masu amfani da lantarkin. Akwai abubuwa da dama da muke yi kuma abubuwa za su fara canzawa.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Ya ce a yanzu ma akwai ci gaba da ake samu a wasu wuraren, amma yanzu ma aka fara samun shawo kan lamura ta yadda ‘yan Nijeriya za su mori lantarki fiye da yadda suke tunani cikin rahusa da kuma inganci a wadace.

Adebayo ya roki ‘yan Nijeriya da su kara hakuri da gwamnatin Tinubu, yana mai cewa halin da ake ciki na wucin gadi ne lamura za su sauya nan ba da jimawa ba.

“Ni kaina na himmatu wajen ganin na shawo kan matsalolin da suke bangaren wutar lantarki, kuma tabbas a kwanan nan ‘yan Nijeriya za su fara rausayawa suna murna da ci gaba da za mu kawo a bangaren,” ya shaida.

Da yake magana kan kokarin gwamnati na shawo kan matsalar karancin mita a Nijeriya, ministan ya ce shugaban kasa ya kafa kwamitin kula da lamuran mita, kuma sun himmatu wajen samar da sama da biliyan 75 domin tabbatar da akalla mita guda miliyan 2 an sanyasu nan da shekaru biyar masu zuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
Kamfanonin Sin Sun Kara Kirkiro Sabbin Kayayyaki Masu Lambar Kira

Kamfanonin Sin Sun Kara Kirkiro Sabbin Kayayyaki Masu Lambar Kira

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.