ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Warware Rikicin Ma’aikata Sama Da 4,000 A Cikin Shekara 8 –Minista

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Minista

Ministan kwadago da samar da ayyuka, Dakta Chris Ngige, ya ce ma’aikatarsa ta warware rikicin ma’aikata kusan 4,000 cikin shekaru takwas.

Ya bayyana hakan ne ga manema labarai na fadar shugaban kasa a lokacin da ya bayyana a taron tattaunawa na mako-mako da kungiyar sadarwa ta shugaban kasa ta shirya a fadar shugaban kasa.

  • Mutum 50 Suka Amfana Da Zakkar Da Wani Bawan Allah Ya Fitar A Kaduna

Ministan wanda ya kare yadda gwamnatin tarayya ke tafiyar da rikice-rikicen ma’aikata, ya ce, “Muna da himma. Mun sasanta rikicin aiki kusan 4,000. Muna samun sanarwar takaddamar ciniki (TDN) kuma muna kiran su don yin taro musamman a masana’antar mai da iskar gas.

ADVERTISEMENT

“Ofisoshinmu na jihohin suna yin sulhu akai-akai”, in ji shi.

Ngige ya kuma bayyana cewa a sakamakon koma- bayan tattalin arzikin kasa ya fuskanta, rashin aikin yi a Nijeriya ya rubanya sama da hudu tun daga shekarar 2015.
Sai dai kuma ya jaddada bukatar yin kokari domin dakile illolin da ke tattare da tattalin arziki da yawan al’ummar kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

“Batutuwa guda uku na rashin aikin yi, talauci da tabarbarewar tattalin arziki sun kasance wani abin damuwa a rayuwar Nijeriya. Adadin rashin aikin yi a kasar ya ninka fiye da sau hudu tun bayan da tattalin arzikin kasar ya fada cikin koma-bayan, na farko a shekarar 2015, sannan kuma a shekarar 2020.

“Yawan rashin aikin yi a Nijeriya ya karu zuwa kashi 9.9 a shekarar 2015 a lokacin da gwamnati mai ci ta zo.
“A cikin ma’anar ILO na rashin aikin yi, akwai bukatar a yi kokari tare dakile illar rashin aikin yi ga tattalin arziki da kuma yawan al’ummar kasar nan.

“A bisa abubuwan da aka ambata kwanan nan ne ya sa gwamnatin tarayya ta kaddamar da wata kungiya mai suna ‘Technical Working Group’ (TWG) a kan samar da ayyukan yi da bunkasa sana’o’in matasa domin tunkarar matsalar rashin aikin yi da bunkasar matasa a kasar nan,” in ji shi.
Dangane da kokarin magance rashin aikin yi, Ngige ya ce kamata ya yi gwamnatin APC mai jiran gado ta yi la’akari da tsarin ofishin samar da ayyukan yi da ke karkashin ma’aikatar kwadago da samar da ayyukan yi.

Ya ce ma’aikatarsa na da cibiyoyin bunkasa fasaha guda 125 a shiyyoyin guda shida na kasar nan, baya ga cibiyoyi 19 na ayyukan yi da ke Bauchi, Kaduna, Legas, Abuja, Edo, da Inugu, da dai sauransu, inda mutane suka samu horo kan aikin samar da bulo.

Ngige ya kuma bayyana cewa ma’aikatarsa na hada kai da ma’aikatar kwadago ta Amurka domin dakile bautar da yara, inda ya kara da cewa sun samar da dala miliyan 75 domin yaki da talauci a yankunan da ake noman koko da ma’adanai a Nijeriya.

Ngige ya ce ana maganar karin albashin ma’aikatan Nijeriya, kuma abin da ke faruwa a yanzu shi ne adadin kudaden da ake samu ya yi karanci ballantana a karin albashi.
Ya kuma ce adadin kudin da za a biya zai dogara ne a kan yadda ake samun kudade da kuma yadda za a iya biya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Shugaban Majalisar Dandalin Asiya Na Boao Ya Yabawa Kiraye-kiraye 3 Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar

Shugaban Majalisar Dandalin Asiya Na Boao Ya Yabawa Kiraye-kiraye 3 Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.