• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Warware Rikicin Ma’aikata Sama Da 4,000 A Cikin Shekara 8 –Minista

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Mun Warware Rikicin Ma’aikata Sama Da 4,000 A Cikin Shekara 8 –Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan kwadago da samar da ayyuka, Dakta Chris Ngige, ya ce ma’aikatarsa ta warware rikicin ma’aikata kusan 4,000 cikin shekaru takwas.

Ya bayyana hakan ne ga manema labarai na fadar shugaban kasa a lokacin da ya bayyana a taron tattaunawa na mako-mako da kungiyar sadarwa ta shugaban kasa ta shirya a fadar shugaban kasa.

  • Mutum 50 Suka Amfana Da Zakkar Da Wani Bawan Allah Ya Fitar A Kaduna

Ministan wanda ya kare yadda gwamnatin tarayya ke tafiyar da rikice-rikicen ma’aikata, ya ce, “Muna da himma. Mun sasanta rikicin aiki kusan 4,000. Muna samun sanarwar takaddamar ciniki (TDN) kuma muna kiran su don yin taro musamman a masana’antar mai da iskar gas.

“Ofisoshinmu na jihohin suna yin sulhu akai-akai”, in ji shi.

Ngige ya kuma bayyana cewa a sakamakon koma- bayan tattalin arzikin kasa ya fuskanta, rashin aikin yi a Nijeriya ya rubanya sama da hudu tun daga shekarar 2015.
Sai dai kuma ya jaddada bukatar yin kokari domin dakile illolin da ke tattare da tattalin arziki da yawan al’ummar kasar.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

“Batutuwa guda uku na rashin aikin yi, talauci da tabarbarewar tattalin arziki sun kasance wani abin damuwa a rayuwar Nijeriya. Adadin rashin aikin yi a kasar ya ninka fiye da sau hudu tun bayan da tattalin arzikin kasar ya fada cikin koma-bayan, na farko a shekarar 2015, sannan kuma a shekarar 2020.

“Yawan rashin aikin yi a Nijeriya ya karu zuwa kashi 9.9 a shekarar 2015 a lokacin da gwamnati mai ci ta zo.
“A cikin ma’anar ILO na rashin aikin yi, akwai bukatar a yi kokari tare dakile illar rashin aikin yi ga tattalin arziki da kuma yawan al’ummar kasar nan.

“A bisa abubuwan da aka ambata kwanan nan ne ya sa gwamnatin tarayya ta kaddamar da wata kungiya mai suna ‘Technical Working Group’ (TWG) a kan samar da ayyukan yi da bunkasa sana’o’in matasa domin tunkarar matsalar rashin aikin yi da bunkasar matasa a kasar nan,” in ji shi.
Dangane da kokarin magance rashin aikin yi, Ngige ya ce kamata ya yi gwamnatin APC mai jiran gado ta yi la’akari da tsarin ofishin samar da ayyukan yi da ke karkashin ma’aikatar kwadago da samar da ayyukan yi.

Ya ce ma’aikatarsa na da cibiyoyin bunkasa fasaha guda 125 a shiyyoyin guda shida na kasar nan, baya ga cibiyoyi 19 na ayyukan yi da ke Bauchi, Kaduna, Legas, Abuja, Edo, da Inugu, da dai sauransu, inda mutane suka samu horo kan aikin samar da bulo.

Ngige ya kuma bayyana cewa ma’aikatarsa na hada kai da ma’aikatar kwadago ta Amurka domin dakile bautar da yara, inda ya kara da cewa sun samar da dala miliyan 75 domin yaki da talauci a yankunan da ake noman koko da ma’adanai a Nijeriya.

Ngige ya ce ana maganar karin albashin ma’aikatan Nijeriya, kuma abin da ke faruwa a yanzu shi ne adadin kudaden da ake samu ya yi karanci ballantana a karin albashi.
Ya kuma ce adadin kudin da za a biya zai dogara ne a kan yadda ake samun kudade da kuma yadda za a iya biya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Sin Ya Jaddada Matsayin Nahiyar Afirka Na Kasancewa A Kan Gaba Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Tsaron Kanta

Next Post

Shugaban Majalisar Dandalin Asiya Na Boao Ya Yabawa Kiraye-kiraye 3 Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar

Related

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

40 minutes ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

4 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

6 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

9 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

10 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

13 hours ago
Next Post
Shugaban Majalisar Dandalin Asiya Na Boao Ya Yabawa Kiraye-kiraye 3 Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar

Shugaban Majalisar Dandalin Asiya Na Boao Ya Yabawa Kiraye-kiraye 3 Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.