ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Warware Rikicin Ma’aikata Sama Da 4,000 A Cikin Shekara 8 –Minista

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Minista

Ministan kwadago da samar da ayyuka, Dakta Chris Ngige, ya ce ma’aikatarsa ta warware rikicin ma’aikata kusan 4,000 cikin shekaru takwas.

Ya bayyana hakan ne ga manema labarai na fadar shugaban kasa a lokacin da ya bayyana a taron tattaunawa na mako-mako da kungiyar sadarwa ta shugaban kasa ta shirya a fadar shugaban kasa.

  • Mutum 50 Suka Amfana Da Zakkar Da Wani Bawan Allah Ya Fitar A Kaduna

Ministan wanda ya kare yadda gwamnatin tarayya ke tafiyar da rikice-rikicen ma’aikata, ya ce, “Muna da himma. Mun sasanta rikicin aiki kusan 4,000. Muna samun sanarwar takaddamar ciniki (TDN) kuma muna kiran su don yin taro musamman a masana’antar mai da iskar gas.

ADVERTISEMENT

“Ofisoshinmu na jihohin suna yin sulhu akai-akai”, in ji shi.

Ngige ya kuma bayyana cewa a sakamakon koma- bayan tattalin arzikin kasa ya fuskanta, rashin aikin yi a Nijeriya ya rubanya sama da hudu tun daga shekarar 2015.
Sai dai kuma ya jaddada bukatar yin kokari domin dakile illolin da ke tattare da tattalin arziki da yawan al’ummar kasar.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

“Batutuwa guda uku na rashin aikin yi, talauci da tabarbarewar tattalin arziki sun kasance wani abin damuwa a rayuwar Nijeriya. Adadin rashin aikin yi a kasar ya ninka fiye da sau hudu tun bayan da tattalin arzikin kasar ya fada cikin koma-bayan, na farko a shekarar 2015, sannan kuma a shekarar 2020.

“Yawan rashin aikin yi a Nijeriya ya karu zuwa kashi 9.9 a shekarar 2015 a lokacin da gwamnati mai ci ta zo.
“A cikin ma’anar ILO na rashin aikin yi, akwai bukatar a yi kokari tare dakile illar rashin aikin yi ga tattalin arziki da kuma yawan al’ummar kasar nan.

“A bisa abubuwan da aka ambata kwanan nan ne ya sa gwamnatin tarayya ta kaddamar da wata kungiya mai suna ‘Technical Working Group’ (TWG) a kan samar da ayyukan yi da bunkasa sana’o’in matasa domin tunkarar matsalar rashin aikin yi da bunkasar matasa a kasar nan,” in ji shi.
Dangane da kokarin magance rashin aikin yi, Ngige ya ce kamata ya yi gwamnatin APC mai jiran gado ta yi la’akari da tsarin ofishin samar da ayyukan yi da ke karkashin ma’aikatar kwadago da samar da ayyukan yi.

Ya ce ma’aikatarsa na da cibiyoyin bunkasa fasaha guda 125 a shiyyoyin guda shida na kasar nan, baya ga cibiyoyi 19 na ayyukan yi da ke Bauchi, Kaduna, Legas, Abuja, Edo, da Inugu, da dai sauransu, inda mutane suka samu horo kan aikin samar da bulo.

Ngige ya kuma bayyana cewa ma’aikatarsa na hada kai da ma’aikatar kwadago ta Amurka domin dakile bautar da yara, inda ya kara da cewa sun samar da dala miliyan 75 domin yaki da talauci a yankunan da ake noman koko da ma’adanai a Nijeriya.

Ngige ya ce ana maganar karin albashin ma’aikatan Nijeriya, kuma abin da ke faruwa a yanzu shi ne adadin kudaden da ake samu ya yi karanci ballantana a karin albashi.
Ya kuma ce adadin kudin da za a biya zai dogara ne a kan yadda ake samun kudade da kuma yadda za a iya biya.

Minista
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Shugaban Majalisar Dandalin Asiya Na Boao Ya Yabawa Kiraye-kiraye 3 Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar

Shugaban Majalisar Dandalin Asiya Na Boao Ya Yabawa Kiraye-kiraye 3 Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.