ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Warware Rikicin Ma’aikata Sama Da 4,000 A Cikin Shekara 8 –Minista

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Minista

Ministan kwadago da samar da ayyuka, Dakta Chris Ngige, ya ce ma’aikatarsa ta warware rikicin ma’aikata kusan 4,000 cikin shekaru takwas.

Ya bayyana hakan ne ga manema labarai na fadar shugaban kasa a lokacin da ya bayyana a taron tattaunawa na mako-mako da kungiyar sadarwa ta shugaban kasa ta shirya a fadar shugaban kasa.

  • Mutum 50 Suka Amfana Da Zakkar Da Wani Bawan Allah Ya Fitar A Kaduna

Ministan wanda ya kare yadda gwamnatin tarayya ke tafiyar da rikice-rikicen ma’aikata, ya ce, “Muna da himma. Mun sasanta rikicin aiki kusan 4,000. Muna samun sanarwar takaddamar ciniki (TDN) kuma muna kiran su don yin taro musamman a masana’antar mai da iskar gas.

ADVERTISEMENT

“Ofisoshinmu na jihohin suna yin sulhu akai-akai”, in ji shi.

Ngige ya kuma bayyana cewa a sakamakon koma- bayan tattalin arzikin kasa ya fuskanta, rashin aikin yi a Nijeriya ya rubanya sama da hudu tun daga shekarar 2015.
Sai dai kuma ya jaddada bukatar yin kokari domin dakile illolin da ke tattare da tattalin arziki da yawan al’ummar kasar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Batutuwa guda uku na rashin aikin yi, talauci da tabarbarewar tattalin arziki sun kasance wani abin damuwa a rayuwar Nijeriya. Adadin rashin aikin yi a kasar ya ninka fiye da sau hudu tun bayan da tattalin arzikin kasar ya fada cikin koma-bayan, na farko a shekarar 2015, sannan kuma a shekarar 2020.

“Yawan rashin aikin yi a Nijeriya ya karu zuwa kashi 9.9 a shekarar 2015 a lokacin da gwamnati mai ci ta zo.
“A cikin ma’anar ILO na rashin aikin yi, akwai bukatar a yi kokari tare dakile illar rashin aikin yi ga tattalin arziki da kuma yawan al’ummar kasar nan.

“A bisa abubuwan da aka ambata kwanan nan ne ya sa gwamnatin tarayya ta kaddamar da wata kungiya mai suna ‘Technical Working Group’ (TWG) a kan samar da ayyukan yi da bunkasa sana’o’in matasa domin tunkarar matsalar rashin aikin yi da bunkasar matasa a kasar nan,” in ji shi.
Dangane da kokarin magance rashin aikin yi, Ngige ya ce kamata ya yi gwamnatin APC mai jiran gado ta yi la’akari da tsarin ofishin samar da ayyukan yi da ke karkashin ma’aikatar kwadago da samar da ayyukan yi.

Ya ce ma’aikatarsa na da cibiyoyin bunkasa fasaha guda 125 a shiyyoyin guda shida na kasar nan, baya ga cibiyoyi 19 na ayyukan yi da ke Bauchi, Kaduna, Legas, Abuja, Edo, da Inugu, da dai sauransu, inda mutane suka samu horo kan aikin samar da bulo.

Ngige ya kuma bayyana cewa ma’aikatarsa na hada kai da ma’aikatar kwadago ta Amurka domin dakile bautar da yara, inda ya kara da cewa sun samar da dala miliyan 75 domin yaki da talauci a yankunan da ake noman koko da ma’adanai a Nijeriya.

Ngige ya ce ana maganar karin albashin ma’aikatan Nijeriya, kuma abin da ke faruwa a yanzu shi ne adadin kudaden da ake samu ya yi karanci ballantana a karin albashi.
Ya kuma ce adadin kudin da za a biya zai dogara ne a kan yadda ake samun kudade da kuma yadda za a iya biya.

Minista
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Shugaban Majalisar Dandalin Asiya Na Boao Ya Yabawa Kiraye-kiraye 3 Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar

Shugaban Majalisar Dandalin Asiya Na Boao Ya Yabawa Kiraye-kiraye 3 Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.