• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Munakisar Da Ke Cikin Batun Tsige Akpabio

…Akpabio Ya Shirya Labarin Tsige Shi Don Hada Fada Tsakanin Tinubu Da Sanatocin Arewa – Sanata Abbo  

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Akpabio
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alamu sun nuna cewa akwai babbar munakisa da ke cikin batun tsige shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da wasu ‘yan majalisa suka yi yunkurin yi.

A cikin wannan makon, fadar shugaban kasa ta fito karara ta nuna cewa ba za ta taba bari a tsige Akpabio ba duk da irin alwashin da wasu ‘yan masalisan suka yi kan batun.

  • An Gabatar Da Rahoton Bunkasuwar Kamfanoni Mallakar Gwamntin Tsakiyar Sin Na 2023

Wata majiya daga fadar shugaban kasa ta shaida wa LEADERSHIP cewa shugaban kasa zai kare kujerar Akpabio yadda ya kamata bisa yunkurin tsige shi idan majalisar dattawa ta koma hutu a karshen wannan watan.

Majiyar ta ce fadar shugaban kasa za ta yi taka-tsan-tsan wajen tsige shugaban majalisar dattawa, domin lamarin na iya haifar da rudani wanda zai iya yaduwa har zuwa majalisar wakilai.

A cewar majiyar, duk da cewa fadar shugaban kasa ba ta ji dadin kalaman da Akpabio ya yi a baya-bayan nan, shugaban kasar na burin ci gaba da mukamin Akpabio ne domin a samu kwanciyar hankali, inda ta kara tabbatar da cewa babu hasashen canjin shugabanci a majalisar dattawan Nijeriya a halin yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Majiyar ta kuma ce fadar shugaban kasa ba za ta yi wasa ba har abokan hamayyar siyasa su yi amfani da wannan dama domin kwace shugabanci a zauren majalisa.

‘Yan majalisun da suka sha kaye da wadanda ba su sami shugabancin kwamiti masu gwabi ba sun yi ta korafe-korafe wanda ake ganin su ne suke ci gaba da ruruta wutar tsige shugaban majalisan.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa kalaman da Akpabio ya yi kan kudin hutun ‘yan majalisa ya sa wasu makarraban Shugaban Tinubu suka fara tunani na neman wanda zai maye gurbin Akpabio.

A karshen makon da ya gabata, LEADERSHIP ta kuma bayar da rahoto na musamman kan yunkurin tsige Akpabio da wasu fusatattun ‘yan majalisa suka yi.

Tuni dai wasu ‘yan majalisa guda biyu daga yankin arewa maso yamma suka jagorantaci wasu sanatoci tattaunawa na yunkurin shirye-shirye aiwatar da tsige shugaban majalisan dattawan.

Fasatattun sun yi zargin cewa shugaban majalisar dattawa ya samu wannan matsayin ne sakamakon goyon bayan shugaban kasa yanzu kuma sun lura cewa ba zai iya gudanar da aikinsa yadda ya kamata ba.

Sai dai shugaban kwamitin majalisar dattawa kan harkokin yada labarai, Yemi Adaramodu, ya yi watsi da barazanar tsige shugaban majalisan. Ya ce wannan yunkurin ne mara tasiri, domin ‘yan majalisar dattawa kan kan su a hade yake.

Ana sa ran majalisan dattawan za ta dawo daga hutu ne a ranar 26 ga Satumba.

Lokacin da aka tuntubi wani dan majalisa wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “An sayar mana da ‘yancinmu ba tare da la’akari da irin nau’yn da ke kanmu ba. Babu wata alkibla da za a amsa daga wurinmu a matsayinmu na ‘yan majalisa.”

Dan majalisar ya ce, “Dangane da abin da ya shafi karamar majalisar, dole ne a fara komai daga fadar shugaban kasa, wanda daga can ne aka hada shugaban majalisar wakilai. Majalisa ta 10 ita ce mafi muni kamar yadda muke iya gani. Mun fi muni fiye da hadin kanmu, ba ma cin gajiyar kanmu a matsayin bangare majalisa masu yin dokoki, sai dai abin da bangaren zartarwa ke so shi ake aiwatarwa.

“Ba labari ne cewa babban mai taimaka wa shugaban kasa da mukarrabansa ne suka hada shugabannin kwamitoci tun daga fadar shugaban kasa, wanda suka danne wadanda ba su so ko wadanda suke ganin suna adawa da Abbas kan rashin ba su kwamitoci masu gwabi.

“Abin takaici ne matuka, domin a majalissar ta 2019, wasun mu sun yi musu tawaye. Ko Wase ya sauka daga layinsu, amma yanzu ga mu nan a jibge. Don haka idan wani abu ya faru da kujerar Akpabio, zai yi tasiri ga Abbas kuma babu wanda zai iya hana shi,” in ji shi.

 

…Akpabio Ya Shirya Labarin Tsige Shi Don Hada Fada Tsakanin Tinubu Da Sanatocin Arewa – Sanata Abbo

 

Dan majalisa mai wakiltar Adamawa ta arewa, Sanata Ishaku Abbo, ya bayyana cewa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ne da kansa ya shirya labarain tsige shi, domin ya kawo sabani tsakanin Tinubu da wasu sanatocin arewa.

Abbo ya kuma kara da cewa shugaban majalisar dattawa ne ya shirya wannan labari domin kawo rashin jituwa tsakanin shugaban kasa Tinubu da wasu ‘yan siyasar arewa.

An dai bayyana cewa Akpabio ya musanta zargin da ake yi masa wanda ya kawo maganar tsige shi. Ya siffanta wadannan rahotanni a matsayin mara tushe balle makama.

An samu rahotanni a kafafen yada labarai a ranar Asabar da ta gabata cewa, ana shirin tsige Akpabio daga shugabancin majalisar dattawa na 10 a lokacin da majalisar za ta koma hutu a ranar 26 ga Satumba, 2023.

Ya ce, “A yau na farka na iske jaridun Nijeriya sama da 10 duk suna dauke da labarin shirin tsige Sanata Akpabio da ‘yan majalisar dattawa daga arewacin Nijeriya ke shirin yi. Har da jaridar Whistler ta anbaci sunan Sanata Abdulaziz Yari da Sanata Aminu Tambuwal da Sanata Ogoshi Onawo da dai sauransu, a matsayin sanatoci da suka yi wannan yunkurin.”

Tun lokacin da Nijeriya ta dawo mulkin dimokuradiyya, tarihi ya nuna cewa zuwa yanzu shugabannin majalisar dattawa biyu ne kacal aka tsige daga mukamansu, yayin da aka tilastama guda daya ya rubuta murabus da kansa ba tare da nuna wata adawa ba.

Wadanda aka tsige sun hada da, Marigayi Sanata Ebans Enwerem da Sanata Chuba Okadigbo. Sannan kuma Sanata Adolfus Wabara ya yi murabus da kansa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

Next Post

Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Akpabio
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.