ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Munakisar Da Ke Cikin Batun Tsige Akpabio

…Akpabio Ya Shirya Labarin Tsige Shi Don Hada Fada Tsakanin Tinubu Da Sanatocin Arewa – Sanata Abbo  

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Akpabio

Alamu sun nuna cewa akwai babbar munakisa da ke cikin batun tsige shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da wasu ‘yan majalisa suka yi yunkurin yi.

A cikin wannan makon, fadar shugaban kasa ta fito karara ta nuna cewa ba za ta taba bari a tsige Akpabio ba duk da irin alwashin da wasu ‘yan masalisan suka yi kan batun.

  • An Gabatar Da Rahoton Bunkasuwar Kamfanoni Mallakar Gwamntin Tsakiyar Sin Na 2023

Wata majiya daga fadar shugaban kasa ta shaida wa LEADERSHIP cewa shugaban kasa zai kare kujerar Akpabio yadda ya kamata bisa yunkurin tsige shi idan majalisar dattawa ta koma hutu a karshen wannan watan.

ADVERTISEMENT

Majiyar ta ce fadar shugaban kasa za ta yi taka-tsan-tsan wajen tsige shugaban majalisar dattawa, domin lamarin na iya haifar da rudani wanda zai iya yaduwa har zuwa majalisar wakilai.

A cewar majiyar, duk da cewa fadar shugaban kasa ba ta ji dadin kalaman da Akpabio ya yi a baya-bayan nan, shugaban kasar na burin ci gaba da mukamin Akpabio ne domin a samu kwanciyar hankali, inda ta kara tabbatar da cewa babu hasashen canjin shugabanci a majalisar dattawan Nijeriya a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

Majiyar ta kuma ce fadar shugaban kasa ba za ta yi wasa ba har abokan hamayyar siyasa su yi amfani da wannan dama domin kwace shugabanci a zauren majalisa.

‘Yan majalisun da suka sha kaye da wadanda ba su sami shugabancin kwamiti masu gwabi ba sun yi ta korafe-korafe wanda ake ganin su ne suke ci gaba da ruruta wutar tsige shugaban majalisan.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa kalaman da Akpabio ya yi kan kudin hutun ‘yan majalisa ya sa wasu makarraban Shugaban Tinubu suka fara tunani na neman wanda zai maye gurbin Akpabio.

A karshen makon da ya gabata, LEADERSHIP ta kuma bayar da rahoto na musamman kan yunkurin tsige Akpabio da wasu fusatattun ‘yan majalisa suka yi.

Tuni dai wasu ‘yan majalisa guda biyu daga yankin arewa maso yamma suka jagorantaci wasu sanatoci tattaunawa na yunkurin shirye-shirye aiwatar da tsige shugaban majalisan dattawan.

Fasatattun sun yi zargin cewa shugaban majalisar dattawa ya samu wannan matsayin ne sakamakon goyon bayan shugaban kasa yanzu kuma sun lura cewa ba zai iya gudanar da aikinsa yadda ya kamata ba.

Sai dai shugaban kwamitin majalisar dattawa kan harkokin yada labarai, Yemi Adaramodu, ya yi watsi da barazanar tsige shugaban majalisan. Ya ce wannan yunkurin ne mara tasiri, domin ‘yan majalisar dattawa kan kan su a hade yake.

Ana sa ran majalisan dattawan za ta dawo daga hutu ne a ranar 26 ga Satumba.

Lokacin da aka tuntubi wani dan majalisa wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “An sayar mana da ‘yancinmu ba tare da la’akari da irin nau’yn da ke kanmu ba. Babu wata alkibla da za a amsa daga wurinmu a matsayinmu na ‘yan majalisa.”

Dan majalisar ya ce, “Dangane da abin da ya shafi karamar majalisar, dole ne a fara komai daga fadar shugaban kasa, wanda daga can ne aka hada shugaban majalisar wakilai. Majalisa ta 10 ita ce mafi muni kamar yadda muke iya gani. Mun fi muni fiye da hadin kanmu, ba ma cin gajiyar kanmu a matsayin bangare majalisa masu yin dokoki, sai dai abin da bangaren zartarwa ke so shi ake aiwatarwa.

“Ba labari ne cewa babban mai taimaka wa shugaban kasa da mukarrabansa ne suka hada shugabannin kwamitoci tun daga fadar shugaban kasa, wanda suka danne wadanda ba su so ko wadanda suke ganin suna adawa da Abbas kan rashin ba su kwamitoci masu gwabi.

“Abin takaici ne matuka, domin a majalissar ta 2019, wasun mu sun yi musu tawaye. Ko Wase ya sauka daga layinsu, amma yanzu ga mu nan a jibge. Don haka idan wani abu ya faru da kujerar Akpabio, zai yi tasiri ga Abbas kuma babu wanda zai iya hana shi,” in ji shi.

 

…Akpabio Ya Shirya Labarin Tsige Shi Don Hada Fada Tsakanin Tinubu Da Sanatocin Arewa – Sanata Abbo

 

Dan majalisa mai wakiltar Adamawa ta arewa, Sanata Ishaku Abbo, ya bayyana cewa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ne da kansa ya shirya labarain tsige shi, domin ya kawo sabani tsakanin Tinubu da wasu sanatocin arewa.

Abbo ya kuma kara da cewa shugaban majalisar dattawa ne ya shirya wannan labari domin kawo rashin jituwa tsakanin shugaban kasa Tinubu da wasu ‘yan siyasar arewa.

An dai bayyana cewa Akpabio ya musanta zargin da ake yi masa wanda ya kawo maganar tsige shi. Ya siffanta wadannan rahotanni a matsayin mara tushe balle makama.

An samu rahotanni a kafafen yada labarai a ranar Asabar da ta gabata cewa, ana shirin tsige Akpabio daga shugabancin majalisar dattawa na 10 a lokacin da majalisar za ta koma hutu a ranar 26 ga Satumba, 2023.

Ya ce, “A yau na farka na iske jaridun Nijeriya sama da 10 duk suna dauke da labarin shirin tsige Sanata Akpabio da ‘yan majalisar dattawa daga arewacin Nijeriya ke shirin yi. Har da jaridar Whistler ta anbaci sunan Sanata Abdulaziz Yari da Sanata Aminu Tambuwal da Sanata Ogoshi Onawo da dai sauransu, a matsayin sanatoci da suka yi wannan yunkurin.”

Tun lokacin da Nijeriya ta dawo mulkin dimokuradiyya, tarihi ya nuna cewa zuwa yanzu shugabannin majalisar dattawa biyu ne kacal aka tsige daga mukamansu, yayin da aka tilastama guda daya ya rubuta murabus da kansa ba tare da nuna wata adawa ba.

Wadanda aka tsige sun hada da, Marigayi Sanata Ebans Enwerem da Sanata Chuba Okadigbo. Sannan kuma Sanata Adolfus Wabara ya yi murabus da kansa.

Akpabio
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
Tambarin Dimokuradiyya

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
Akpabio
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Next Post
Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

LABARAI MASU NASABA

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.