ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Munakisar Da Ke Cikin Batun Tsige Akpabio

…Akpabio Ya Shirya Labarin Tsige Shi Don Hada Fada Tsakanin Tinubu Da Sanatocin Arewa – Sanata Abbo  

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Akpabio

Alamu sun nuna cewa akwai babbar munakisa da ke cikin batun tsige shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da wasu ‘yan majalisa suka yi yunkurin yi.

A cikin wannan makon, fadar shugaban kasa ta fito karara ta nuna cewa ba za ta taba bari a tsige Akpabio ba duk da irin alwashin da wasu ‘yan masalisan suka yi kan batun.

  • An Gabatar Da Rahoton Bunkasuwar Kamfanoni Mallakar Gwamntin Tsakiyar Sin Na 2023

Wata majiya daga fadar shugaban kasa ta shaida wa LEADERSHIP cewa shugaban kasa zai kare kujerar Akpabio yadda ya kamata bisa yunkurin tsige shi idan majalisar dattawa ta koma hutu a karshen wannan watan.

ADVERTISEMENT

Majiyar ta ce fadar shugaban kasa za ta yi taka-tsan-tsan wajen tsige shugaban majalisar dattawa, domin lamarin na iya haifar da rudani wanda zai iya yaduwa har zuwa majalisar wakilai.

A cewar majiyar, duk da cewa fadar shugaban kasa ba ta ji dadin kalaman da Akpabio ya yi a baya-bayan nan, shugaban kasar na burin ci gaba da mukamin Akpabio ne domin a samu kwanciyar hankali, inda ta kara tabbatar da cewa babu hasashen canjin shugabanci a majalisar dattawan Nijeriya a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Majiyar ta kuma ce fadar shugaban kasa ba za ta yi wasa ba har abokan hamayyar siyasa su yi amfani da wannan dama domin kwace shugabanci a zauren majalisa.

‘Yan majalisun da suka sha kaye da wadanda ba su sami shugabancin kwamiti masu gwabi ba sun yi ta korafe-korafe wanda ake ganin su ne suke ci gaba da ruruta wutar tsige shugaban majalisan.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa kalaman da Akpabio ya yi kan kudin hutun ‘yan majalisa ya sa wasu makarraban Shugaban Tinubu suka fara tunani na neman wanda zai maye gurbin Akpabio.

A karshen makon da ya gabata, LEADERSHIP ta kuma bayar da rahoto na musamman kan yunkurin tsige Akpabio da wasu fusatattun ‘yan majalisa suka yi.

Tuni dai wasu ‘yan majalisa guda biyu daga yankin arewa maso yamma suka jagorantaci wasu sanatoci tattaunawa na yunkurin shirye-shirye aiwatar da tsige shugaban majalisan dattawan.

Fasatattun sun yi zargin cewa shugaban majalisar dattawa ya samu wannan matsayin ne sakamakon goyon bayan shugaban kasa yanzu kuma sun lura cewa ba zai iya gudanar da aikinsa yadda ya kamata ba.

Sai dai shugaban kwamitin majalisar dattawa kan harkokin yada labarai, Yemi Adaramodu, ya yi watsi da barazanar tsige shugaban majalisan. Ya ce wannan yunkurin ne mara tasiri, domin ‘yan majalisar dattawa kan kan su a hade yake.

Ana sa ran majalisan dattawan za ta dawo daga hutu ne a ranar 26 ga Satumba.

Lokacin da aka tuntubi wani dan majalisa wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “An sayar mana da ‘yancinmu ba tare da la’akari da irin nau’yn da ke kanmu ba. Babu wata alkibla da za a amsa daga wurinmu a matsayinmu na ‘yan majalisa.”

Dan majalisar ya ce, “Dangane da abin da ya shafi karamar majalisar, dole ne a fara komai daga fadar shugaban kasa, wanda daga can ne aka hada shugaban majalisar wakilai. Majalisa ta 10 ita ce mafi muni kamar yadda muke iya gani. Mun fi muni fiye da hadin kanmu, ba ma cin gajiyar kanmu a matsayin bangare majalisa masu yin dokoki, sai dai abin da bangaren zartarwa ke so shi ake aiwatarwa.

“Ba labari ne cewa babban mai taimaka wa shugaban kasa da mukarrabansa ne suka hada shugabannin kwamitoci tun daga fadar shugaban kasa, wanda suka danne wadanda ba su so ko wadanda suke ganin suna adawa da Abbas kan rashin ba su kwamitoci masu gwabi.

“Abin takaici ne matuka, domin a majalissar ta 2019, wasun mu sun yi musu tawaye. Ko Wase ya sauka daga layinsu, amma yanzu ga mu nan a jibge. Don haka idan wani abu ya faru da kujerar Akpabio, zai yi tasiri ga Abbas kuma babu wanda zai iya hana shi,” in ji shi.

 

…Akpabio Ya Shirya Labarin Tsige Shi Don Hada Fada Tsakanin Tinubu Da Sanatocin Arewa – Sanata Abbo

 

Dan majalisa mai wakiltar Adamawa ta arewa, Sanata Ishaku Abbo, ya bayyana cewa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ne da kansa ya shirya labarain tsige shi, domin ya kawo sabani tsakanin Tinubu da wasu sanatocin arewa.

Abbo ya kuma kara da cewa shugaban majalisar dattawa ne ya shirya wannan labari domin kawo rashin jituwa tsakanin shugaban kasa Tinubu da wasu ‘yan siyasar arewa.

An dai bayyana cewa Akpabio ya musanta zargin da ake yi masa wanda ya kawo maganar tsige shi. Ya siffanta wadannan rahotanni a matsayin mara tushe balle makama.

An samu rahotanni a kafafen yada labarai a ranar Asabar da ta gabata cewa, ana shirin tsige Akpabio daga shugabancin majalisar dattawa na 10 a lokacin da majalisar za ta koma hutu a ranar 26 ga Satumba, 2023.

Ya ce, “A yau na farka na iske jaridun Nijeriya sama da 10 duk suna dauke da labarin shirin tsige Sanata Akpabio da ‘yan majalisar dattawa daga arewacin Nijeriya ke shirin yi. Har da jaridar Whistler ta anbaci sunan Sanata Abdulaziz Yari da Sanata Aminu Tambuwal da Sanata Ogoshi Onawo da dai sauransu, a matsayin sanatoci da suka yi wannan yunkurin.”

Tun lokacin da Nijeriya ta dawo mulkin dimokuradiyya, tarihi ya nuna cewa zuwa yanzu shugabannin majalisar dattawa biyu ne kacal aka tsige daga mukamansu, yayin da aka tilastama guda daya ya rubuta murabus da kansa ba tare da nuna wata adawa ba.

Wadanda aka tsige sun hada da, Marigayi Sanata Ebans Enwerem da Sanata Chuba Okadigbo. Sannan kuma Sanata Adolfus Wabara ya yi murabus da kansa.

Akpabio
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

MASU ALAKA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

LABARAI MASU NASABA

ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

July 20, 2026
Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

July 20, 2026
Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

July 20, 2026
Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

July 20, 2026
Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

July 19, 2026
Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

July 19, 2026
Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.