ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

by Muhammad
3 years ago
Kano

Wani hatsarin mota da ya afku a garin Zakirai da ke kan hanyar Kano zuwa Ringim a karamar hukumar Gabasawa a jihar Kano, ya ci rayukan fasinjoji 18.

Lamarin da ya faru a sakamakon makare wata mota da lodin kaya, ya hada da wasu motocin kasuwanci guda biyu, inda ya yi taho mu gama da wata motar bas.

  • Fasinjoji 14 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Kano – FRSC 
  • Mutum 3 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Kano

Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya tabbatar da afkuwar hatsarin.

ADVERTISEMENT

Ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Juma’a.

“Mun samu waya game da hadarin da misalin karfe 8:35 na dare a ranar Juma’a kuma muka tura jami’an mu wurin domin ceto wadanda abin ya shafa,” inji shi.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

“Hatsarin ya rutsa da fasinjoji 35 a cikin motocin bas guda biyu, daga ciki 18 sun kone kurmus, yayin da wasu 12 suka samu munanan raunuka.”

Da yake jajantawa, Abdullahi ya koka game da yawaitar samun hadurran a jihar Kano cikin makon da ya gabata.

A ziyarar da ya kai wurin da hatsarin ya afku a ranar Asabar, ya gargadi masu ababen hawa, musamman masu zirga-zirgar ababen hawa da na jahohi, da su guji wuce gona da iri yayin tuki.

An garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano domin samun kulawar gaggawa.

A halin da ake ciki, an yi jana’izar wasu da suka mutu a wurin da hatsarin ya afku, yayin da wasu kuma aka mika su ga ‘yan uwansu.

Bisa la’akari da yawaitar hadurran kan tituna a baya-bayan nan, hukumar FRSC ta yi alkawarin kara wayar da kan jama’a tare da tabbatar da tsauraran matakan tsaro.

Waɗannan yunƙurin sun haɗa da aikin kotunan tafi-da-gidanka don ladabtar da masu karya ka’idojin tuki cikin gaggawa da tabbatar da bin ka’idojin kiyaye hanya.

An yi kira ga masu ababen hawa da su ba da fifiko ga tsaro, da kuma guje wa wuce gona da iri yayin tuki da duk wani yunkuri da ka iya kawo hatsari ga kansu da sauran mutane a kan hanya.

Al’umar yankin da mahukunta sun yi matukar alhinin asarar rayukan da aka samu a wannan mummunan hatsarin, kuma sun ci alwashin tsayawa tsayin daka a kokarinsu na hana afkuwar hadura a kan tituna.

Kano
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami'ai Kan Gurbata Muhalli

LABARAI MASU NASABA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.