• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

by Muhammad
4 months ago
in Manyan Labarai
0
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani hatsarin mota da ya afku a garin Zakirai da ke kan hanyar Kano zuwa Ringim a karamar hukumar Gabasawa a jihar Kano, ya ci rayukan fasinjoji 18.

Lamarin da ya faru a sakamakon makare wata mota da lodin kaya, ya hada da wasu motocin kasuwanci guda biyu, inda ya yi taho mu gama da wata motar bas.

  • Fasinjoji 14 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Kano – FRSC 
  • Mutum 3 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Kano

Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya tabbatar da afkuwar hatsarin.

Ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Juma’a.

“Mun samu waya game da hadarin da misalin karfe 8:35 na dare a ranar Juma’a kuma muka tura jami’an mu wurin domin ceto wadanda abin ya shafa,” inji shi.

Labarai Masu Nasaba

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

Shekara 100 Da Kafa IAR: Da Sakamakon Bincikenmu Aka Kafa Ginshikin Tattalin Arzikin Arewacin Nijeriya —Farfesa Ishiyaku

“Hatsarin ya rutsa da fasinjoji 35 a cikin motocin bas guda biyu, daga ciki 18 sun kone kurmus, yayin da wasu 12 suka samu munanan raunuka.”

Da yake jajantawa, Abdullahi ya koka game da yawaitar samun hadurran a jihar Kano cikin makon da ya gabata.

A ziyarar da ya kai wurin da hatsarin ya afku a ranar Asabar, ya gargadi masu ababen hawa, musamman masu zirga-zirgar ababen hawa da na jahohi, da su guji wuce gona da iri yayin tuki.

An garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano domin samun kulawar gaggawa.

A halin da ake ciki, an yi jana’izar wasu da suka mutu a wurin da hatsarin ya afku, yayin da wasu kuma aka mika su ga ‘yan uwansu.

Bisa la’akari da yawaitar hadurran kan tituna a baya-bayan nan, hukumar FRSC ta yi alkawarin kara wayar da kan jama’a tare da tabbatar da tsauraran matakan tsaro.

Waɗannan yunƙurin sun haɗa da aikin kotunan tafi-da-gidanka don ladabtar da masu karya ka’idojin tuki cikin gaggawa da tabbatar da bin ka’idojin kiyaye hanya.

An yi kira ga masu ababen hawa da su ba da fifiko ga tsaro, da kuma guje wa wuce gona da iri yayin tuki da duk wani yunkuri da ka iya kawo hatsari ga kansu da sauran mutane a kan hanya.

Al’umar yankin da mahukunta sun yi matukar alhinin asarar rayukan da aka samu a wannan mummunan hatsarin, kuma sun ci alwashin tsayawa tsayin daka a kokarinsu na hana afkuwar hadura a kan tituna.

Tags: GabasawaHatsarin Motakano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Next Post

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Related

BUA
Manyan Labarai

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

11 hours ago
Shekara 100 Da Kafa IAR: Da Sakamakon Bincikenmu Aka Kafa Ginshikin Tattalin Arzikin Arewacin Nijeriya —Farfesa Ishiyaku
Manyan Labarai

Shekara 100 Da Kafa IAR: Da Sakamakon Bincikenmu Aka Kafa Ginshikin Tattalin Arzikin Arewacin Nijeriya —Farfesa Ishiyaku

18 hours ago
Batun Yadda Samari Ke Barin Taimakon Iyaye Su Kashe Wa ‘Yan Mata Kudi
Madubin Rayuwa

Batun Yadda Samari Ke Barin Taimakon Iyaye Su Kashe Wa ‘Yan Mata Kudi

19 hours ago
Kano
Manyan Labarai

Jawabin Shugaba Tinubu Kan Cikar Nijeriya Shekaru 63 Da Samun ‘Yancin Kai

21 hours ago
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Manyan Labarai

NLC Da TUC Na Hada Kan Ma’aikata Don Tafka Gagarumin Yajin Aiki

1 day ago
Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Jaddada Aniyar Magance Rashin Tsaro Da Talauci A Nijeriya

1 day ago
Next Post
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami'ai Kan Gurbata Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

Dambe: An Fafata Tsakanin Dan Aliyu Da Rabe Shagon Ebola

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.