ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

by Muhammad
3 years ago
Kano

Wani hatsarin mota da ya afku a garin Zakirai da ke kan hanyar Kano zuwa Ringim a karamar hukumar Gabasawa a jihar Kano, ya ci rayukan fasinjoji 18.

Lamarin da ya faru a sakamakon makare wata mota da lodin kaya, ya hada da wasu motocin kasuwanci guda biyu, inda ya yi taho mu gama da wata motar bas.

  • Fasinjoji 14 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Kano – FRSC 
  • Mutum 3 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Kano

Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya tabbatar da afkuwar hatsarin.

ADVERTISEMENT

Ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Juma’a.

“Mun samu waya game da hadarin da misalin karfe 8:35 na dare a ranar Juma’a kuma muka tura jami’an mu wurin domin ceto wadanda abin ya shafa,” inji shi.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

“Hatsarin ya rutsa da fasinjoji 35 a cikin motocin bas guda biyu, daga ciki 18 sun kone kurmus, yayin da wasu 12 suka samu munanan raunuka.”

Da yake jajantawa, Abdullahi ya koka game da yawaitar samun hadurran a jihar Kano cikin makon da ya gabata.

A ziyarar da ya kai wurin da hatsarin ya afku a ranar Asabar, ya gargadi masu ababen hawa, musamman masu zirga-zirgar ababen hawa da na jahohi, da su guji wuce gona da iri yayin tuki.

An garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano domin samun kulawar gaggawa.

A halin da ake ciki, an yi jana’izar wasu da suka mutu a wurin da hatsarin ya afku, yayin da wasu kuma aka mika su ga ‘yan uwansu.

Bisa la’akari da yawaitar hadurran kan tituna a baya-bayan nan, hukumar FRSC ta yi alkawarin kara wayar da kan jama’a tare da tabbatar da tsauraran matakan tsaro.

Waɗannan yunƙurin sun haɗa da aikin kotunan tafi-da-gidanka don ladabtar da masu karya ka’idojin tuki cikin gaggawa da tabbatar da bin ka’idojin kiyaye hanya.

An yi kira ga masu ababen hawa da su ba da fifiko ga tsaro, da kuma guje wa wuce gona da iri yayin tuki da duk wani yunkuri da ka iya kawo hatsari ga kansu da sauran mutane a kan hanya.

Al’umar yankin da mahukunta sun yi matukar alhinin asarar rayukan da aka samu a wannan mummunan hatsarin, kuma sun ci alwashin tsayawa tsayin daka a kokarinsu na hana afkuwar hadura a kan tituna.

Kano
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

MASU ALAKA

Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi
Manyan Labarai

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa
Manyan Labarai

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba
Manyan Labarai

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Next Post
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami'ai Kan Gurbata Muhalli

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

September 15, 2026
Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

September 15, 2026
’Yan Ta’adda Sun Kai Wa Ƙauyuka 2 Hari A Adamawa

Boko Haram Sun Kashe Mutane 4 Tare Da Ƙone Gidaje A Adamawa

September 15, 2026
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Arziƙin Dangote Ya Haura Dala Biliyan 50 Bayan Fara Sayar Da Hannun Jarin Matatarsa – Forbes

September 15, 2026
Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

September 14, 2026
Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

September 14, 2026
Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

September 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.