ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

by Muhammad
3 years ago
Kano

Wani hatsarin mota da ya afku a garin Zakirai da ke kan hanyar Kano zuwa Ringim a karamar hukumar Gabasawa a jihar Kano, ya ci rayukan fasinjoji 18.

Lamarin da ya faru a sakamakon makare wata mota da lodin kaya, ya hada da wasu motocin kasuwanci guda biyu, inda ya yi taho mu gama da wata motar bas.

  • Fasinjoji 14 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Kano – FRSC 
  • Mutum 3 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Kano

Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya tabbatar da afkuwar hatsarin.

ADVERTISEMENT

Ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Juma’a.

“Mun samu waya game da hadarin da misalin karfe 8:35 na dare a ranar Juma’a kuma muka tura jami’an mu wurin domin ceto wadanda abin ya shafa,” inji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

“Hatsarin ya rutsa da fasinjoji 35 a cikin motocin bas guda biyu, daga ciki 18 sun kone kurmus, yayin da wasu 12 suka samu munanan raunuka.”

Da yake jajantawa, Abdullahi ya koka game da yawaitar samun hadurran a jihar Kano cikin makon da ya gabata.

A ziyarar da ya kai wurin da hatsarin ya afku a ranar Asabar, ya gargadi masu ababen hawa, musamman masu zirga-zirgar ababen hawa da na jahohi, da su guji wuce gona da iri yayin tuki.

An garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano domin samun kulawar gaggawa.

A halin da ake ciki, an yi jana’izar wasu da suka mutu a wurin da hatsarin ya afku, yayin da wasu kuma aka mika su ga ‘yan uwansu.

Bisa la’akari da yawaitar hadurran kan tituna a baya-bayan nan, hukumar FRSC ta yi alkawarin kara wayar da kan jama’a tare da tabbatar da tsauraran matakan tsaro.

Waɗannan yunƙurin sun haɗa da aikin kotunan tafi-da-gidanka don ladabtar da masu karya ka’idojin tuki cikin gaggawa da tabbatar da bin ka’idojin kiyaye hanya.

An yi kira ga masu ababen hawa da su ba da fifiko ga tsaro, da kuma guje wa wuce gona da iri yayin tuki da duk wani yunkuri da ka iya kawo hatsari ga kansu da sauran mutane a kan hanya.

Al’umar yankin da mahukunta sun yi matukar alhinin asarar rayukan da aka samu a wannan mummunan hatsarin, kuma sun ci alwashin tsayawa tsayin daka a kokarinsu na hana afkuwar hadura a kan tituna.

Kano
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

June 12, 2026
Kano
Manyan Labarai

June 12, 2026
Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya
Manyan Labarai

Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya

June 12, 2026
Next Post
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami'ai Kan Gurbata Muhalli

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.