ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

by Malumfashi Ibrahim Muhammad S Balogun
3 years ago
Rubutun Hausa

Dukkan abubuwan da suka faru a baya za a ga daidaikun mutane ne ke yi da kulawar hukuma, sai dai hukumar ba ta sa baki ba sosai da sosai sai a shekarar 1955 da aka kafa Hukumar Kula Da Lamurran Hausa, (Hausa Language Board) wadda hukuma ce da ta yi kokarin daidaita Hausa da samar da ka’idojin rubuta Hausar.

Hukumar ta yi abubuwa da dama, ita ce ta gyara da tantance duk wadansu kalmomin aro da na kimiyya da fasaha. Wannan hukuma ce kuma ta waiwayi aikin da Hans Bischer ya yi domin daidaita tunani da zamani, ta samar da kundin da ta kira Rules for Hausa Orthography a 1958.

  • Sin Ta Jaddada Kira Ga Sassan Masu Ruwa Da Tsaki A Rikicin Sudan Da Su Gaggauta Dakatar Da Bude Wuta

A daidai wannan lokaci ne aka tsayar da karin Hausar Kano a matsayin Daidaitacciyar Hausa, sai dai an shelanta cewa duk inda aka sami kalmomi da a cikin garin Kano kadai ake furta su, ana iya maye gurbinsu da wadansu daga kare-karen Hausa can daban da suka fi karbuwa.

ADVERTISEMENT

Bayan da Turawan mulkin mallaka suka bar kasar Hausa, an yi ta kokari daga ‘yan gida a daidaita rubutun Hausa. Taro na farko da aka yi shi ne a birnin Bamako na kasar Mali a shekarar 1966, karkashin jagorancin Hukumar UNESCO, inda aka tattauna yadda za a daidaita rubutun Hausa a Yammacin Afrirka. A wannan taron ne aka amince a rubuta Hausa kamar haka:
Haruffa masu lankwasa /b/ da /k/ da /d/ kamar yadda suke yanzu.
Aka samar da tagwayen haruffa /sh/ da /ts/ da /gy/ da /ky/ da /ky/ da /gw/ da /kw/.
A kuma raba /su/ da /na/ wato /su na/ ko /ka na/ ko /ki na/ da /ya na/ dss.
A shekarar 1970 kuma an yi wani taron a jami’ar Ahmadu Bello, Zaria inda aka sake kallon aikin da Hukumar Kula Da Lamurran Hausa ta yi a 1958, aka samar da sababbin bayanai kamar haka:
A dinga rubuta /ko’ina/ ba /ko ina/ ba
Haka a rubuta /yake/ ba /ya ke/ ba, ko /yakan/ ba /ya kan/ ba, /suna/ ba /su na/ ba.
Da kuma /mutum/ ba /mutun/ ba
Da /malam/ ba /malan/ ba
/Ranar kasuwa/ ba /ranak kasuwa/ ba.
A shekarar 1972 kuma an sake gudanar da wani taro a a jami’ar Bayero Kano, wanda shi ma ya yi kokarin daidaita ka’idojin rubutun Hausa, an amince da ‘yan gyare-gyare da dama, wadanda za iya cewa su ne har yau ake amfani da su a duk fadin duniyar Hausa.
Ga kadan daga abubuwan da aka amince da su a wurin taron, kamar yadda Farfesa M.K.M.Galadanci ya kattaba:
Universal nouns are written as one word:
/komai/ ba /ko mai/ ba
/kowa/ ba /ko wa/ ba
/koyaushe/ ba /ko yaushe/ ba.

Where the pre-berbal pronoun precedes the tense marker it is written as one word:
/yakan/ ba /ya kan/ ba
/yana/ ba /ya na/ ba.
Where the tense marker precedes the pre-berbal pronoun it is written separately: /za mu/ ba /zamu/ ba.
/za su/ ba /zasu ba.
A short possessibe is joined to the preceding nominal:
/dokina/ ba /doki na/ ba
/rigarsa/ ba /rigar sa/ ba
/zanenta/ ba /zanen ta/ ba.

LABARAI MASU NASABA

Goron Juma’a

GORON JUMA’A 22-05-2026

But the long possessibe is written separately:
/wani doki nawa/ ba /wani dokinawa/ ba
/wata riga tawa/ ba /wata rigatawa/ ba
/wani zane nata/ ba /wani zanenata/ ba.

The pronoun object is written separately:
/ya ba ni/ ba /ya bani/ ba.
/mun sa shi/ ba /mun sashi/ ba
/ana kiran ka/ ba /ana kiranka/ ba.

Haka kuma an jaddada cewa /saboda/ da /watakila/ kalmomi ne a cure wuri guda, ba a rubuta su a ware ba, wato /sabo da/ ko /wata kila/ ba da sauran su.

Taron karshe da aka yi na daidaita rubutun Hausa shi ne wanda aka yi a Niamey, a kasar Nijar a shekarar 1980, karkashin jagorancin Kungiyar Hada Kan Afirka, (OAU). An shirya wannan taro ne don a mayar da hankali wajen daidaita rubutun Hausa a Nijeriya da Nijar, shi ma wannan taro ya amince da muhimman bayanai da suka hada da:
Tabbatar da gajerun wasullan Hausa: i,e,a,o,u.
Tabbatar da dogayen wasullan Hausa: ii,ee,aa,oo,uu.
Da kuma bakaken Hausa kuda 33.
Daga lokacin da aka rushe Hausa Language Board (Hukumar Kula Da Lamurran Hausa) da aka kafa a 1958 sai aka mayar da yawancin ayyukanta ga Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya da ke karkashin Jami’ar Bayero, Kano, ita ce mai kula da ka’idoji da daidaita rubutun Hausa, kuma tun daga 1982 ta yi iyakacin kokarinta na yin wannan aiki tukuru.

Ita ce ke shirya tarurrukan inganta harsunan Nijeriya (musamman na Hausa da Fulfulde da Kanuri). Ta kuma samar da aikin fassara kalmomin zamani zuwa Hausa da kuma Kamusun Hausa cikin Hausa da ta buga a shekarar 2007, bayan sama da shekara 30 ana bincike da nazari da bita.

Haka batun Daidaitacciyar Hausa ya kasance a cikin tsawon tarihi, sai dai an gudanar da ‘yan kwarya-kwaryan tarurruka nan da can domin jawo hankali kan sake zama na musamman game da yadda za a sake bitar halin da ake ciki game da sababbin da tsofaffin matsaloli da ke jibge a tsawon zamani, sai dai da yake ba tarurrukan a-zo-a-gani ba ne ba a cimma matsaya a hukumance ba.

Domin ganin an shawo kan wannan lamari, Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyyar Harshe na Jami’ar Jihar Kaduna a shekarar 2019 ya shirya taron kasa da kasa domin sake bitar batutuwan da suka shafi daidaitacciyar Hausa da ka’idojin rubutun Hausa don sake samar da matsaya.

Taron da ya samu halarcin masana daga sassa daban-daban na duniya, an kuma kawo batutuwa da ake ganin matsaloli ne aka tattauna su. An kuma gabatar da makaloli daban-daban da suka shafi lamurran da ke ci wa fagen tuwo a kwarya.
Kamar yadda aka saba game da tarurruka irin wadannan, an sake zama na musamman a shekarar 2021 a NTI, Kaduna, karkashin jagorancin Sashen Harsunan Nijeriya Da Kimiyyar Harshe na Jami’ar Jihar Kaduna, inda aka zakulo masana da malamai da dalibai daga sassa daban-daban domin yin matsaya bisa ga abubuwan da aka tattauna a taron Kaduna na 2019, game da ka’idojin rubutun Hausa a karni na 21.

Taron ya yi armashi, domin Farfesoshi da Daktoci sama da 40 suka yi wa batutuwan da aka zo da su daga taron 2019 turgeza, aka samar da matsaya da za a iya kiran ta da matsayar taron KASU, KADUNA 2021!
Inda muke ke nan a halin yanzu, sai dai abin da zan kara a nan shi ne, a wadannan tarurruka biyu na 2019 da 2021 da aka yi a Kaduna, kusan dukkan wadanda ke da ra’ayi da ya saba wanda ake da shi a hukumance ba wanda ya zo ko suka taro domin wakiltar su, don jin me ya jawo adawa da matsayar da ake da ita, da su, suke da ita. Duk da haka wannan bai hana an tattauna matsalolin da ra’ayoyin masu adawar da su, an kuma yi matsaya, a ilmance ba!

Rubutun Hausa
Malumfashi Ibrahim Muhammad S Balogun
+ postsBio

    MASU ALAKA

    GORON JUMA’A 17-04-2026
    Goron Juma'a

    Goron Juma’a

    June 5, 2026
    GORON JUMA’A 01-07-2025
    Goron Juma'a

    GORON JUMA’A 22-05-2026

    May 22, 2026
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
    Labarai

    Ku Kula Da Kyawawan Ɗabi’u, Su Ne Waɗanda Annabi SAW Ya Kira Duk Halitta A Kansu

    April 17, 2026
    Next Post
    Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

    Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

    LABARAI MASU NASABA

    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

    June 12, 2026
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

    June 12, 2026
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

    June 12, 2026
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

    June 12, 2026
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

    June 12, 2026
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

    June 12, 2026
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

    June 12, 2026
    Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

    Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

    June 12, 2026
    Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

    Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

    June 12, 2026
    Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

    Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa

    June 12, 2026

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

    No Result
    View All Result
    • Gida
    • Labarai
      • Manyan Labarai
      • Kananan Labarai
      • Masarautu
      • Bakon Marubuci
      • Dausayin Musulunci
      • Daga Kasar Sin
      • Nishadi
      • Noma Da Kiwo
      • Sana’a Sa’a
      • Tambarin Dimokuradiyya
      • Taskira
      • Daga Birnin Sin
      • Ado Da Kwalliya
    • Siyasa
    • Wasanni
    • Al’adu
    • Al’ajabi
    • Labaran Kasuwanci
    • Karanta cikin Turanci

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.