• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 17 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Ekiti

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Mutum 17 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Garkuwa Da Mutane A Ekiti
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yan sandan Jihar Ekiti ta gurfanar da wasu mutane 17 da ake zargi da aikata laifuka a jihar tare da kwato wasu makamai a hannunus.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ogundare Dare, ya ce rundunar ta kama mutanen da ake zargi da aikata laifuka daban-daban.

  • Yanzu-yanzu: Tsohon gwamnan Anambra, Mbadinuju Ya Rasu
  • El-Rufai Ya Jinjina Wa Sojoji Kan Kashe Kasurgumin Dan Bindiga, Danwasa A Kaduna

Da ta ke gabatar da wadanda ake zargin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Sunday Abutu, ta ce rundunar ‘yan sandan ta RRS a ranar 6 ga watan Afrilu, ta hanyar kai farmakin daji, sun kama wani Augustine Agboobo, Adeniyi Olamilekan, Williams Ukeuima Friday da Ademoh Gabriel, a cikin dajin da ke kusa da yankin gonakin Igede.

“A yayin da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun amsa cewa su ‘yan kungiyar masu garkuwa da mutane ne da suka gudanar da ayyukan garkuwa da mutane a jihar Ekiti ciki har da sace Ajibade Adeleke a gonar Igede da kuma karbar kudin fansa wasu”.

Abutu ta kara da cewa rundunar ta kama wasu mutane biyu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne tare da hadin gwiwar wasu al’umma a Oke-Ureje da ke Ado-Ekiti a ranar 4 ga watan Afrilu da misalin karfe 22:00 sannan ta kama Saliu Oyebamiji da Ajisefe Mayowa.

Labarai Masu Nasaba

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Haka kuma, an kama wani fitaccen dan fashi da makami mai suna Jimoh Gani a ranar 4 ga watan Afrilu, bisa laifin yin fashi da makami da yi wa wata dalibar Jami’a fyade a Ikere-Ekiti.

“Lokacin da ake yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.”

Rundunar ta kwato kayayyaki daban-daban da suka hada da bindigar gida daya, bindigar maharba guda daya da buhun tabar wiwi da sauransu.

Rundunar ‘yan sandan ta yi kira ga daukacin ‘yan kasar nan da su kula da harkokin tsaro tare da kai rahoton duk wani abu da ya faru a yankinsu ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SandaFashi Da MakamiLaifukaZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fasinjoji 12 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ebonyi

Next Post

Abba Gida-Gida Bai Cancanci Zama Gwamnan Kano Ba –APC

Related

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

48 minutes ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

3 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

5 hours ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

5 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

7 hours ago
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
Labarai

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

9 hours ago
Next Post
Abba Gida-Gida Bai Cancanci Zama Gwamnan Kano Ba –APC

Abba Gida-Gida Bai Cancanci Zama Gwamnan Kano Ba –APC

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.