Kwamishinan lafiya na Jihar Bauchi Dakta Adamu Sambo, ya ce an samu barkewar cutar Sankarau wato meningitis (CSM) har guda shida a fadin jihar.
Kwamishinan ya ba da tabbacin ne a lokacin da aka masa tambaya dangane da barkewar cutar Sankarau a jihar da ke makwabtaka da Bauchi wato jihar Yobe.
- “Tsadar Kayan Gini Zai Haifar Da Karuwar Rugujewar Gine-gine”
- Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Layin Dogo Da Kamfanin Sin Ya Gina A Legas
Ya ce’m: “Eh, muna da CSM. Mun samu guda 6 da aka tabbatar a sassa daban-daban na jihar.”
Sai dai kuma, gwamnatin jihar ta ba da tabbacin daukan matakan da suka dace wajen ganin ta dakile yaduwar cutar Sankarau a fadin jihar baki daya.
Matakan da gwamnatin ta fara dauka na magance yaduwar cutar sun fi karfi a arewacin jihar yankunan da suka hada iyaka da jihar Yobe wato Gamawa, Dambam, Zaki, Katagum da kuma karamar hukumar Itas/Gadau.
Wani ma’aikacin hukumar kula da lafiya a matakin farko na jihar Bauchi da ya roki a sakaye sunansa, ya tabbatar da cewa akwai barkewar cutar a wasu kananan hukumomin da ke arewacin jihar sai dai na shi ne ke da ikon shelanta wa duniya hakan ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp