Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Na Shirya Kalubalantar Barcelona A Kotu – Neymar

by
2 years ago
in WASANNI
2 min read
Neymar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Abba Ibrahim Wada

Dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German kuma na tawagar kasar Brazil, Neymar, ya bayyana cewa ya shirya kalubalantar kungiyar Barcelona a gaban kotu bayan da tsohuwar kungiyar tasa ta bayyana cewa zata kaishi kotu akan ya karbi albashi a kungiyar sama da yadda yakamata ya karba.

A satin daya gabata ne Barcelona tace zata gurfanar da tsohon dan wasanta Neymar a gaban kotu saboda abinda ta kira biyan sa kudaden da suka wuce kima da suka kai Dala miliyan 12 lokacin da yake bugawa kungiyar wasa.

Labarai Masu Nasaba

Ban Fitar Da Ran Bugawa Real Madrid Wasa Ba A Nan Gaba, Cewar Mbappe

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

Jaridar El Mundo da ake wallafawa a kasar ta Sipaniya ta ruwaito cewar Neymar da yayi wasa a kungiyar Barcelona tsakanin shekarar 2013 zuwa 2017 ya karbi kudaden da suka wuce kima daga kungiyar a matsayin albashi.

Rahotanni sun ce dan wasan na Brazil na daga cikin sahun farko na ‘yan wasan da suka kaucewa biyan haraji a Spain, inda ake bin sa bashin sama da yuro 34 da rabi wanda hakan tasa har hukumomin kasar suka gurfanar dashi a gaban kotu.

Hukumomin Spain na kuma gudanar da bincike kan lokacin da Neymar yaje Barcelona da kuma tafiyar sa PSG sannan wata Kotu a Spain ta bukaci Neymar da ya biya Barcelona yuro miliyan 6 da dubu 790,000.

ADVERTISEMENT

“Ban san abinda yake faruwa sai dai kawai in karanta a jarida kuma naga rahoton cewa zasu kaini kotu akan sun biyani kudade saboda haka ina mai sanar dasu cewar a shirye nake dana kalubalanci ikirarinsu a gaban kotu” in ji Neymar

Ya cigaba da cewa “Duk irin zargin da sukeyi inada hujjar d azan iya kare kaina saboda abune mukayi a rubuce cikin yarjejeniya da wakilaina su ma kuma a matsayinsu na kungiya da nasu wakilan babu wanda a ka yi wani abu a tsakaninmu ba tare daya amince ba”

A shekarun da suka gabata dai Barcelona taso ta sake sayan dan wasan daga PSG sai dai daga baya cinikin bai kasance ba sakamakon kudin da PSG ta bukata Barcelona ba zata iya biya ba kuma tun kafin bullar cutar Korona ma.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Hadin Kai Ne Kadai Hanya Daya Tilo Ta Raya Moriyar Sin Da Amurka

Next Post

Mascherano Ya Yi Ritaya Daga Buga Kwallo

Labarai Masu Nasaba

Ban Fitar Da Ran Bugawa Real Madrid Wasa Ba A Nan Gaba, Cewar Mbappe

Ban Fitar Da Ran Bugawa Real Madrid Wasa Ba A Nan Gaba, Cewar Mbappe

by Abba Ibrahim Wada
23 hours ago
0

...

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

by
4 days ago
0

...

Chiellini

Chiellini Ya Bar Juventus

by Abba Ibrahim Wada
5 days ago
0

...

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
2 weeks ago
0

...

Next Post
Mascherano

Mascherano Ya Yi Ritaya Daga Buga Kwallo

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: