• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Gargadi Alhazai Su Guji Tsarabar Ruwan Zamzam 

by Bello Hamza
12 months ago
in Labarai
0
NAHCON Ta Gargadi Alhazai Su Guji Tsarabar Ruwan Zamzam 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON ta gargadi Alhazai da su guji debo ruwan Zamzam a matsayin tsaraba a yayin da suke shirye-shiryen dawowa gida Nijeriya.

Daraktan tsare-tsare na hukumar, Prince Anofi Olanrewaju Elegushi ya sanar da haka a yayin da yake ganawa da Alhazan Jihar Ogun a Tantinsu da ke Muna ta Saudiyya, inda ya ce, hukumar Saudiya ta haramta wa Alhazai jigilar Ruwan Zamzam a mastayin tsaraba zuwa gida Nijeriya, “Maimakon haka hukumar Alhazai ta NAHCON ta yi shirin kai wa duk wani Alhajin Nijeriya, ruwan zamzama lita 5 zuwa gida wanda zai karba da zaran ya sauka a filin jirgin sama” , “Dibar ruwan zamzama a cikin kayan Alhazai yana iya barazana ga yanayin tafiyar jirgin sama a sararin samaniya, saboda hada duk wanda aka kama ya debo ruwan zamzam zai fuskanci fushin hukuma, “ in ji shi.

Ya kuma nemi Alhazai su bi dokar kayyade kaya da aka tanada na kilo 8 a jakar hannu da kuma kilo 32 a babbar jaka, “Dauko kayan da suka wuce wadannan ka’ida na iya sa mutum ya yi asarar kayayyakin gaba daya”, a kan haka ya nemi Alhazai su yi hattara wajen sayen kayayyaki domin kada su jibgo kayan da suka wuce kima.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin

Daga nan ya taya Alhazan murnar kammala aikin Hajji cikin nasara, ya ce, “Dole a yaba da halayyar kirki da Alhazan suka nuna a zaman su na Muna, Arafat da Muzdalifah, musamman ganin ba a samu wata hayaniya ko rikici ba a wannan karon kamar yadda yake faruwa a baya”, ya kuma nemi Alhazan su guji abubuwan da za su iya bada musu aikin su, ya kuma nuna muhimmanci dore wa da darussan da aikin Hajji ke koyarwa a cikin harkokin rayuwar su na yau da kullum, ya ce, dole Alhaji ko Hajiya su kare mutuncin wannan matsayin da Allah ya ba su a rayuwa.

A ziyarar, Prince Anofi Olanrewaju Elegushi wanda ya jagoranci wasu manyan ma’aikatan NAHCON da suka hada da Hajiya Zainab Musa da Dakta Tajudeen A. Oladejo da Farfesa Adedimeji M. Adebola da Alidu Shuttu da Babatunde Odunola da kuma Injiniya Goni Sanda Mohammed, sun ziyarci Tantin Alhazan jihohin Legas da Ogun da Ondo da Osun da Oyo da Kwara da kuma Ekiti, a dukkan inda aka ziyarta Alhazai sun yi tambayoyi inda Prince Anofi Olanrewaju Elegushi ya warware musu amsoshin tambayoyin nasu, tambayoyin da aka fi yi a dukkan jihohin da aka ziyarta sun ta’allaka ne ga yadda Alhazai ba su samu cikakken kudin guzuri na Dala 500 ba kamar yadda suka biya tun a gida Nijeriya sun kuma nemi a samar da karin matsugunnai a Muna, Muzdalifah da Arafat.

Labarai Masu Nasaba

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

A martanins,a ya dora laifin rashin samun kudin guzuri bai daya a kan yadda farashin Dala ke tashi da kuma yadda darajar Naira take faduwa a kullum. Ya kuma nemi Alhazan su yi hakuri da yadda lamarin ya kasance.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlhazaiHajjin BanaZam-Zam
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Wadatar Kayan Aiki: Yadda Nijeriya Ta Kasa Dakatar Da Asarar Naira Tiriliyan 1.4 A Sashen Kiwon Lafiya

Next Post

Abubuwa Biyu Da Suka Fi Daukar Hankali A Hajjin Bana

Related

Ministan Tsaro
Labarai

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

35 minutes ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 hour ago
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya
Labarai

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

3 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

3 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

4 hours ago
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

12 hours ago
Next Post
Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (II)

Abubuwa Biyu Da Suka Fi Daukar Hankali A Hajjin Bana

LABARAI MASU NASABA

Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.