• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAHCON Ta Gargadi Alhazai Su Guji Tsarabar Ruwan Zamzam 

by Bello Hamza
1 year ago
Alhazai

Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON ta gargadi Alhazai da su guji debo ruwan Zamzam a matsayin tsaraba a yayin da suke shirye-shiryen dawowa gida Nijeriya.

Daraktan tsare-tsare na hukumar, Prince Anofi Olanrewaju Elegushi ya sanar da haka a yayin da yake ganawa da Alhazan Jihar Ogun a Tantinsu da ke Muna ta Saudiyya, inda ya ce, hukumar Saudiya ta haramta wa Alhazai jigilar Ruwan Zamzam a mastayin tsaraba zuwa gida Nijeriya, “Maimakon haka hukumar Alhazai ta NAHCON ta yi shirin kai wa duk wani Alhajin Nijeriya, ruwan zamzama lita 5 zuwa gida wanda zai karba da zaran ya sauka a filin jirgin sama” , “Dibar ruwan zamzama a cikin kayan Alhazai yana iya barazana ga yanayin tafiyar jirgin sama a sararin samaniya, saboda hada duk wanda aka kama ya debo ruwan zamzam zai fuskanci fushin hukuma, “ in ji shi.

Ya kuma nemi Alhazai su bi dokar kayyade kaya da aka tanada na kilo 8 a jakar hannu da kuma kilo 32 a babbar jaka, “Dauko kayan da suka wuce wadannan ka’ida na iya sa mutum ya yi asarar kayayyakin gaba daya”, a kan haka ya nemi Alhazai su yi hattara wajen sayen kayayyaki domin kada su jibgo kayan da suka wuce kima.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin

Daga nan ya taya Alhazan murnar kammala aikin Hajji cikin nasara, ya ce, “Dole a yaba da halayyar kirki da Alhazan suka nuna a zaman su na Muna, Arafat da Muzdalifah, musamman ganin ba a samu wata hayaniya ko rikici ba a wannan karon kamar yadda yake faruwa a baya”, ya kuma nemi Alhazan su guji abubuwan da za su iya bada musu aikin su, ya kuma nuna muhimmanci dore wa da darussan da aikin Hajji ke koyarwa a cikin harkokin rayuwar su na yau da kullum, ya ce, dole Alhaji ko Hajiya su kare mutuncin wannan matsayin da Allah ya ba su a rayuwa.

A ziyarar, Prince Anofi Olanrewaju Elegushi wanda ya jagoranci wasu manyan ma’aikatan NAHCON da suka hada da Hajiya Zainab Musa da Dakta Tajudeen A. Oladejo da Farfesa Adedimeji M. Adebola da Alidu Shuttu da Babatunde Odunola da kuma Injiniya Goni Sanda Mohammed, sun ziyarci Tantin Alhazan jihohin Legas da Ogun da Ondo da Osun da Oyo da Kwara da kuma Ekiti, a dukkan inda aka ziyarta Alhazai sun yi tambayoyi inda Prince Anofi Olanrewaju Elegushi ya warware musu amsoshin tambayoyin nasu, tambayoyin da aka fi yi a dukkan jihohin da aka ziyarta sun ta’allaka ne ga yadda Alhazai ba su samu cikakken kudin guzuri na Dala 500 ba kamar yadda suka biya tun a gida Nijeriya sun kuma nemi a samar da karin matsugunnai a Muna, Muzdalifah da Arafat.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

A martanins,a ya dora laifin rashin samun kudin guzuri bai daya a kan yadda farashin Dala ke tashi da kuma yadda darajar Naira take faduwa a kullum. Ya kuma nemi Alhazan su yi hakuri da yadda lamarin ya kasance.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC
Labarai

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Next Post
Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (II)

Abubuwa Biyu Da Suka Fi Daukar Hankali A Hajjin Bana

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.