Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASASHEN WAJE

Nahiyar Turai: Jemima Layzell: Yarinyar Da Ta Kyautar Da Sassan Jikinta

by Tayo Adelaja
September 11, 2017
in KASASHEN WAJE
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Abin mamaki baya karewa a wannan duniyar. Wata yarinya ‘yar shekara 13 da ta mutu sakamakon cutar kumburin jijiyar kwakwalwa, ta taimaka wurin bayar da gudummawar sassan jikinta ga mutum takwas, adadi mafi yawa a tarihi.

Jemima Layzell, wacce ‘yar asalin yankin Somerset ce da ke London, ta rasu a 2012, ta bayar da gudummawar zuciya, tumburkuma, huhu, kodoji, karamin hanji da hanta ga yara biyar.

samndaads

Iyayen Jemima sun ce marigayiyar na da basira da tausayi kuma Allah ya ba ta fikira – a dalilin haka ne ma suke matukar alfahari da wannan abin tarihi da ta aikata.

Hukumomin lafiya sun ce babu wani mutum da ya taba bayar da gudummawa ga mutane da yawa kamar Jemima.

An yiwa mutum uku dashen zuciya da ‘yan hanji da tumburkumarta a lokaci guda kuma mutum biyu suka samu kodojinta.

An raba hantarta inda aka dasawa mutum biyu, sannan kuma wani mara lafiya ya samu gudummawar huhunan da ta bari.

Akasari dai, ba a cika samun irin wannan gudummawa ga adadin mutane masu yawa haka ba.

‘Ta musamman ce kuma ba irinta’

Mahaifiyar Jemima, Sophy Layzell, mai shekara 43, kuma mai koyar da wasannin kwaikwayo da mahaifinta Harbey Layzell, dan shekara 49, kuma manajan darakta a wani kamfanin gine-gine, sun ce sun san Jemima na son ta bayar da gudummawar sassan jikinta. Saboda sun yi magana akan haka kwanaki kalilan kafin mutuwarta, bayan wani mutum da suka sani yayi hatsari ya mutu.

Sophy ta ce Jemima ba ta taba jin batun bayar da gudummawar sashen jiki ba kafin wannan lokaci, kuma ta yi ta dar-dar, amma dai ta fahimci muhimmanci abin.”

Ta ce har yanzu suna jin bayar da gudummawar sassan jikin ‘yarsu, shawara ce mai wahala amma dai ita ce daidai.

A cewarta idan muka ce a’a, tamkar mun hana wa sauran mutum takwas damar rayuwa. Duk iyaye suna iya cewa a’a, don kuwa Allah ya yi mu ne mu kare ‘ya’yanmu. Kawai dai mun kwan da sanin cewa Jemima ta amince a yi hakan shi ya sa muka ce eh.

Cibiyar kula da ayyukan dashe da karin jiki ta shirin inshorar lafiya a Ingila ta ce daruruwan mutane ne har yanzu ke mutuwa ba gaira ba dalili a lokacin da suke jiran a yi musu dashe, don kuwa iyaye da dama suna kin bayar da gudummawa.

Rahoton kafar BBC ya nakalto cewa; A bara, mutum 457 ne suka mutu lokacin da suke jiran samun dashe a cikinsu 14 kananan yara ne. A yanzu haka akwai mutum 6,414 da ke cikin jerin wadanda ke jiran samun gudummawa kuma sun hada da yara 176.

A shekara ta 2015, wani matashi da ya mutu Tom Wilson mai shekara 22 sakamakon tsurewar da ya yi bayan sandar kwallon hockey ta same shi a ka. An kiyasta cewa gudummawar sassan jikinsa da ya bayar, ciki har da fata da kashi da bargo ta taimaka wa rayuwar kimanin mutum 50.

 

 

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Zaben 2019: Gwamnoni Da Ministoci Na Goyon Bayan Buhari Ya Zarce —Gwamna El-rufai

Next Post

Bakon Marubuci: Tunasarwa Game Da Matsalar Daba A Siyasa (1)

RelatedPosts

Faduwar Trump

Me Zai Biyo Bayan Darewar Karajar Biden Da Faduwar Trump?

by Muhammad
5 days ago
0

Idanun duniya na kan ranar Larabar jiya, 20 ga Janarairu,...

Rigakafi

An Soma Yin Allurar Korona A India Da Brazil

by Muhammad
5 days ago
0

A yau asabar kasashen Duniya da suka hada Indiya ,Brazil...

Trump Ya Fice Daga Fadar ‘White House’ Gabanin Rantsar Da Biden

Trump Ya Fice Daga Fadar ‘White House’ Gabanin Rantsar Da Biden

by Muhammad
5 days ago
0

Trump ya ce mutane "ba su san aiki tukuru" da...

Next Post

Bakon Marubuci: Tunasarwa Game Da Matsalar Daba A Siyasa (1)

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version