• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Naja'atu

A halin da ake ciki kuma, Kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar APC ya mayar da martani kan bayanan Naja’atu kan watsi da dan takararsu na shugaban kasa Bola Tinubu, inda kwamitin ya ce Naja’atu Mohammed cikin banci ce a wurinsu wanda hakan ya sa suka kore ta.

Ya ce Naja’atu ta kasance tsohuwar daraktar hulda da kungiyoyin fararen hula a cikin kwamitin yakin neman zaben APC, amma saboda rashin kwarewa da fadace-fadace ne ya sa suka kore ta.

  • Kaso Mai Tsoka Na Ra’ayoyin Jama’a Ya Nuna Gamsuwa Da Nasarar Kasar Sin A Fannin Kandagarkin COVID-19
  • Karancin Man Fetur Da Sauya Kudade Shiri Ne Na Hana Zaben 2023 —Tinubu

A ranar 19 ga watan Janairun 2023, Naja’atu ta mika wasikar ajiye aiki ga shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Adamu, inda ta bayyana cewa ta ajiye mukaminta sakamakon matsalolin da Nijeriya ke fuskanta tana bukatar ci gaba da fafutukar samun ingantacciyar kasa.

Amma a cikin wata sanarwa da mashawarci kan harkokin da suka shafi jama’a na yakin neman zaben APC, Mahmud Jega ya fitar, ya ce Naja’atu tana yaudarar ‘yan Nijeriya cewa ita da kanta ta ajiye aiki bayan kuma korar ta aka yi daga kwamitin yakin neman zaben na APC.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, Jega ya ce, “Tawagar yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu/Shettima ba ta samu takardar Naja’atu Mohammed na ajiye mukaminta a matsayin daraktar hulda da kungiyoyin fararen hula ba kafin a kore ta sakamakon rashin kwarewa da fadace-fadace, bayan ta yi watsi da gargadinmu na bai wa abokan adawa bayanan sirri.

LABARAI MASU NASABA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

“Duk da ta kasance tana yaudarar ‘yan Nijeriya da cewa ita da kanta ta ajiye mukamin, wasikar korarta tana nan kan teburinta a ofishinta. Ta kasance cikon banci, tun lokacin da aka kore ta daga yakin neman zabe, take ta sambatu.

“Ta kasance ‘yar siyasa mara akida da take takama da kwarewa kuma ba ta da ita, kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na APC yana mamakin yadda Naja’atu wacce ta kasance ba likita ba amma take shakkun lafiyar Tinubu bayan likitoci sun tabbatar da cewa zai iya yin mulkin Nijeriya.

“Ko kungiyar likitoci za su kori magananta bisa zantar da hukuncin kan lafiya ba tare da yin gwaji ba.

“Duk da shi ne dan takarar shugaban kasa a 2023 da ya fi sauran ganin nasara a bayyana, amma Tinubu ya ziyarci mafi yawancin sassan kasar nan domin yin gaggamin yakin neman zabe da ganawa da kwararru da al’ummomi da kungiyoyin ‘yan kasuwa da kungiyoyin addinai,” in ji Jega.

Ya kara da cewa maganar da Naja’atu take yi cewa lokacin da ta tambayi Tinubu shirin da ya yi wa ‘yan arewa, sai ya ce bai da shi, wannan zance kawai ne.

“Tinubu yana da kyakkyawan tsari kan kasar nan, musamman matsalolin da suka shafi arewa. Lokacin da Tinubu ya halarci taron gamayyar kungiyoyin arewa a shekarar da ta gabata, ya bayyana musu irin abubuwan da ya tanada wa arewa.

“Muna kira ga magoya bayanmu a dukkan kasar nan su yi watsi da duk wata suka ga tafiyar Tinubu/Shettima ga ‘yan siyasa mara ka’ida.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)
Manyan Labarai

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Next Post
Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

LABARAI MASU NASABA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.