• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Da Sin Abokai Ne Dake Haifarwa Juna Da Alfanu

by Sulaiman
4 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Najeriya Da Sin Abokai Ne Dake Haifarwa Juna Da Alfanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hausawa su kan ce, da abokin daka a kan sha gari. A ganina, wannan karin magana ya bayyana yanayin huldar dake tsakanin Sin da Najeriya. Matukar an lura da hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen 2, to, za a rika ganin labarai masu kyau a kai a kai.

Za mu iya daukar wasu abubuwan da suka faru a kwanan nan a matsayin misali. Da farko dai, a karshen bara, babban bankin kasar Sin da babban bankin Nijeriya, sun sabunta yarjejeniyarsu ta musayar kudaden kasashensu da jimillarsu ta kai RMB yuan biliyan 15, ko kuma kudin Nijeriya kimanin Naira tiriliyan 3 da biliyan 280, inda aka samu wani sabon wa’adin yarjejeniyar na shekaru 3. Hakan zai fadada amfani da kudin kasa a cikin gida tsakanin Sin da Nijeriya, da saukaka harkokin cinikayya, da zuba jari, da hadin kai a fannin hada-hadar kudi tsakanin sassan biyu, da tinkarar kalubalen hawa da saukar darajar musayar kudi a kasuwannin kasa da kasa.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Majalisar Dokokin Legas Ta Tsige Kakakinta
  • Gwamnan Zamfara Ya Jajanta Wa Iyalan Da Harin Jirgin Sojoji Ya Rutsa Da Su

Na biyu shi ne, a kwanan baya, bankin CDB na kasar Sin ya samar da rance a zangon farko, wanda yawansa ya kai Euro miliyan 245, domin ci gaba da aikin gina layin dogo tsakanin jihohin Kaduna da Kano na arewacin Najeriya. Wani kamfanin kasar Sin ne ke daukar nauyin shimfida layin dogon da tsawonsa ya kai kilomita 203, wanda zai saukaka tafiye-tafiyen al’ummar arewacin Najeriya, bayan da aka kammala aikin ginin layin dogon.

Na uku shi ne, karuwar cinikayyar da ake yi tsakanin Sin da Najeriya, ta sa wani kamfanin jigilar kayayyaki ta jiragen ruwa na kasa da kasa ya kaddamar da wani layin jigilar kaya kai tsaye tsakanin birnin Shanghai na Sin da Lagos na Najeriya, a farkon watan da muke ciki. Layin zai takaita lokacin jigilar kaya tsakanin biranen 2 zuwa kwanaki 27, kana farashin hidimar jigilar kayan ma ya ragu.

A sa’i daya kuma, manyan jami’an kasashen 2 suna cudanya da juna sosai. Misali, a kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya kammala ziyararsa a Najeriya. Sa’an nan a jiya, darekata janar mai kula da huldar abota tsakanin Najeriya da Sin, wadda ta shafi manyan tsare-tsare a dukkan fannoni na tarayyar Najeriya, Joseph Tegbe, shi ma ya isa birnin Beijing na Sin, inda ya fara wata ziyara a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Watakila za ka so ka san dalilin da ya sa ake samun cudanya sosai tsakanin Sin da Najeriya, kana huldar dake tsakaninsu na da kyau matuka?

Dalili na farko shi ne, kamar yadda ministan wajen kasar Najeriya, Yusuf Tuggar ya fada, yayin da yake ganawa da Mista Wang Yi a wannan karo, wato “Ba wani bambancin ra’ayi tsakanin Najeriya da Sin.” Hakika, kasashen Najeriya da Sin, bisa matsayinsu na manyan kasashe da tattalin arzikinsu ke kan hanyar ci gaba, suna da buri iri daya, wato zamanantar da kansu, da kyautata zaman rayuwar jama’a. Kana sam ba sa sha’awar ra’ayin kasashen yamma na ja-in-ja a fannin siyasa a duniya.

Ban da haka, Najeriya da Sin suna da moriya ta bai daya. Inda kasar Sin ke kokarin hada manufofin raya kasa da ta gabatar, da shirin raya tattalin arziki na Najeriya, don biyan bukatun Najeriya na samun ci gaba, da tabbatar da moriyar kamfanonin Sin a lokaci guda.

A nan gaba, yayin da ake kokarin gina yankin ciniki mai ‘yanci na nahiyar Afirka, Najeriya a bisa matsayinta na babbar kasa, da tattalin arziki mai karfi, tabbas za ta iya amfani da fifikonta a fannonin kayayyakin more rayuwa, da albarkatun kasa, da fasahohi, gami da jari, wajen jagorantar aikin cin gajiyar kasuwannin yankin da take ciki. Yayin da hadin gwiwar Sin da Najeriya zai iya taimakon Najeriya wajen taka muhimmiyar rawa a fannin raya yankin da take ciki, tare da haifar wa kamfanonin Sin masu zuba jari da riba. Tabbas wannan makoma mai haske, ita ce babban dalilin da ya sa ake samun dangantaka mai kyau tsakanin Najeriya da Sin. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-ɗumi: Majalisar Dokokin Legas Ta Tsige Kakakinta

Next Post

Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin Safarar Yara A Filato

Related

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

1 day ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

3 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

4 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

5 days ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
Ra'ayi Riga

Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba

2 weeks ago
Next Post
Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin  Safarar Yara A Filato

Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin Safarar Yara A Filato

LABARAI MASU NASABA

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

May 12, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.