• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Da Sin Abokai Ne Dake Haifarwa Juna Da Alfanu

by Sulaiman
8 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Najeriya Da Sin Abokai Ne Dake Haifarwa Juna Da Alfanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hausawa su kan ce, da abokin daka a kan sha gari. A ganina, wannan karin magana ya bayyana yanayin huldar dake tsakanin Sin da Najeriya. Matukar an lura da hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen 2, to, za a rika ganin labarai masu kyau a kai a kai.

Za mu iya daukar wasu abubuwan da suka faru a kwanan nan a matsayin misali. Da farko dai, a karshen bara, babban bankin kasar Sin da babban bankin Nijeriya, sun sabunta yarjejeniyarsu ta musayar kudaden kasashensu da jimillarsu ta kai RMB yuan biliyan 15, ko kuma kudin Nijeriya kimanin Naira tiriliyan 3 da biliyan 280, inda aka samu wani sabon wa’adin yarjejeniyar na shekaru 3. Hakan zai fadada amfani da kudin kasa a cikin gida tsakanin Sin da Nijeriya, da saukaka harkokin cinikayya, da zuba jari, da hadin kai a fannin hada-hadar kudi tsakanin sassan biyu, da tinkarar kalubalen hawa da saukar darajar musayar kudi a kasuwannin kasa da kasa.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Majalisar Dokokin Legas Ta Tsige Kakakinta
  • Gwamnan Zamfara Ya Jajanta Wa Iyalan Da Harin Jirgin Sojoji Ya Rutsa Da Su

Na biyu shi ne, a kwanan baya, bankin CDB na kasar Sin ya samar da rance a zangon farko, wanda yawansa ya kai Euro miliyan 245, domin ci gaba da aikin gina layin dogo tsakanin jihohin Kaduna da Kano na arewacin Najeriya. Wani kamfanin kasar Sin ne ke daukar nauyin shimfida layin dogon da tsawonsa ya kai kilomita 203, wanda zai saukaka tafiye-tafiyen al’ummar arewacin Najeriya, bayan da aka kammala aikin ginin layin dogon.

Na uku shi ne, karuwar cinikayyar da ake yi tsakanin Sin da Najeriya, ta sa wani kamfanin jigilar kayayyaki ta jiragen ruwa na kasa da kasa ya kaddamar da wani layin jigilar kaya kai tsaye tsakanin birnin Shanghai na Sin da Lagos na Najeriya, a farkon watan da muke ciki. Layin zai takaita lokacin jigilar kaya tsakanin biranen 2 zuwa kwanaki 27, kana farashin hidimar jigilar kayan ma ya ragu.

A sa’i daya kuma, manyan jami’an kasashen 2 suna cudanya da juna sosai. Misali, a kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya kammala ziyararsa a Najeriya. Sa’an nan a jiya, darekata janar mai kula da huldar abota tsakanin Najeriya da Sin, wadda ta shafi manyan tsare-tsare a dukkan fannoni na tarayyar Najeriya, Joseph Tegbe, shi ma ya isa birnin Beijing na Sin, inda ya fara wata ziyara a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Watakila za ka so ka san dalilin da ya sa ake samun cudanya sosai tsakanin Sin da Najeriya, kana huldar dake tsakaninsu na da kyau matuka?

Dalili na farko shi ne, kamar yadda ministan wajen kasar Najeriya, Yusuf Tuggar ya fada, yayin da yake ganawa da Mista Wang Yi a wannan karo, wato “Ba wani bambancin ra’ayi tsakanin Najeriya da Sin.” Hakika, kasashen Najeriya da Sin, bisa matsayinsu na manyan kasashe da tattalin arzikinsu ke kan hanyar ci gaba, suna da buri iri daya, wato zamanantar da kansu, da kyautata zaman rayuwar jama’a. Kana sam ba sa sha’awar ra’ayin kasashen yamma na ja-in-ja a fannin siyasa a duniya.

Ban da haka, Najeriya da Sin suna da moriya ta bai daya. Inda kasar Sin ke kokarin hada manufofin raya kasa da ta gabatar, da shirin raya tattalin arziki na Najeriya, don biyan bukatun Najeriya na samun ci gaba, da tabbatar da moriyar kamfanonin Sin a lokaci guda.

A nan gaba, yayin da ake kokarin gina yankin ciniki mai ‘yanci na nahiyar Afirka, Najeriya a bisa matsayinta na babbar kasa, da tattalin arziki mai karfi, tabbas za ta iya amfani da fifikonta a fannonin kayayyakin more rayuwa, da albarkatun kasa, da fasahohi, gami da jari, wajen jagorantar aikin cin gajiyar kasuwannin yankin da take ciki. Yayin da hadin gwiwar Sin da Najeriya zai iya taimakon Najeriya wajen taka muhimmiyar rawa a fannin raya yankin da take ciki, tare da haifar wa kamfanonin Sin masu zuba jari da riba. Tabbas wannan makoma mai haske, ita ce babban dalilin da ya sa ake samun dangantaka mai kyau tsakanin Najeriya da Sin. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-ɗumi: Majalisar Dokokin Legas Ta Tsige Kakakinta

Next Post

Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin Safarar Yara A Filato

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

4 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 week ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 week ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

1 week ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

1 week ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 weeks ago
Next Post
Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin  Safarar Yara A Filato

Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin Safarar Yara A Filato

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.