ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Da Sin Abokai Ne Dake Haifarwa Juna Da Alfanu

by Sulaiman
2 years ago
Sin

Hausawa su kan ce, da abokin daka a kan sha gari. A ganina, wannan karin magana ya bayyana yanayin huldar dake tsakanin Sin da Najeriya. Matukar an lura da hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen 2, to, za a rika ganin labarai masu kyau a kai a kai.

Za mu iya daukar wasu abubuwan da suka faru a kwanan nan a matsayin misali. Da farko dai, a karshen bara, babban bankin kasar Sin da babban bankin Nijeriya, sun sabunta yarjejeniyarsu ta musayar kudaden kasashensu da jimillarsu ta kai RMB yuan biliyan 15, ko kuma kudin Nijeriya kimanin Naira tiriliyan 3 da biliyan 280, inda aka samu wani sabon wa’adin yarjejeniyar na shekaru 3. Hakan zai fadada amfani da kudin kasa a cikin gida tsakanin Sin da Nijeriya, da saukaka harkokin cinikayya, da zuba jari, da hadin kai a fannin hada-hadar kudi tsakanin sassan biyu, da tinkarar kalubalen hawa da saukar darajar musayar kudi a kasuwannin kasa da kasa.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Majalisar Dokokin Legas Ta Tsige Kakakinta
  • Gwamnan Zamfara Ya Jajanta Wa Iyalan Da Harin Jirgin Sojoji Ya Rutsa Da Su

Na biyu shi ne, a kwanan baya, bankin CDB na kasar Sin ya samar da rance a zangon farko, wanda yawansa ya kai Euro miliyan 245, domin ci gaba da aikin gina layin dogo tsakanin jihohin Kaduna da Kano na arewacin Najeriya. Wani kamfanin kasar Sin ne ke daukar nauyin shimfida layin dogon da tsawonsa ya kai kilomita 203, wanda zai saukaka tafiye-tafiyen al’ummar arewacin Najeriya, bayan da aka kammala aikin ginin layin dogon.

ADVERTISEMENT

Na uku shi ne, karuwar cinikayyar da ake yi tsakanin Sin da Najeriya, ta sa wani kamfanin jigilar kayayyaki ta jiragen ruwa na kasa da kasa ya kaddamar da wani layin jigilar kaya kai tsaye tsakanin birnin Shanghai na Sin da Lagos na Najeriya, a farkon watan da muke ciki. Layin zai takaita lokacin jigilar kaya tsakanin biranen 2 zuwa kwanaki 27, kana farashin hidimar jigilar kayan ma ya ragu.

A sa’i daya kuma, manyan jami’an kasashen 2 suna cudanya da juna sosai. Misali, a kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya kammala ziyararsa a Najeriya. Sa’an nan a jiya, darekata janar mai kula da huldar abota tsakanin Najeriya da Sin, wadda ta shafi manyan tsare-tsare a dukkan fannoni na tarayyar Najeriya, Joseph Tegbe, shi ma ya isa birnin Beijing na Sin, inda ya fara wata ziyara a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Watakila za ka so ka san dalilin da ya sa ake samun cudanya sosai tsakanin Sin da Najeriya, kana huldar dake tsakaninsu na da kyau matuka?

Dalili na farko shi ne, kamar yadda ministan wajen kasar Najeriya, Yusuf Tuggar ya fada, yayin da yake ganawa da Mista Wang Yi a wannan karo, wato “Ba wani bambancin ra’ayi tsakanin Najeriya da Sin.” Hakika, kasashen Najeriya da Sin, bisa matsayinsu na manyan kasashe da tattalin arzikinsu ke kan hanyar ci gaba, suna da buri iri daya, wato zamanantar da kansu, da kyautata zaman rayuwar jama’a. Kana sam ba sa sha’awar ra’ayin kasashen yamma na ja-in-ja a fannin siyasa a duniya.

Ban da haka, Najeriya da Sin suna da moriya ta bai daya. Inda kasar Sin ke kokarin hada manufofin raya kasa da ta gabatar, da shirin raya tattalin arziki na Najeriya, don biyan bukatun Najeriya na samun ci gaba, da tabbatar da moriyar kamfanonin Sin a lokaci guda.

A nan gaba, yayin da ake kokarin gina yankin ciniki mai ‘yanci na nahiyar Afirka, Najeriya a bisa matsayinta na babbar kasa, da tattalin arziki mai karfi, tabbas za ta iya amfani da fifikonta a fannonin kayayyakin more rayuwa, da albarkatun kasa, da fasahohi, gami da jari, wajen jagorantar aikin cin gajiyar kasuwannin yankin da take ciki. Yayin da hadin gwiwar Sin da Najeriya zai iya taimakon Najeriya wajen taka muhimmiyar rawa a fannin raya yankin da take ciki, tare da haifar wa kamfanonin Sin masu zuba jari da riba. Tabbas wannan makoma mai haske, ita ce babban dalilin da ya sa ake samun dangantaka mai kyau tsakanin Najeriya da Sin. (Bello Wang)

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin  Safarar Yara A Filato

Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin Safarar Yara A Filato

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.