ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Da Sin Abokai Ne Dake Haifarwa Juna Da Alfanu

by Sulaiman
1 year ago
Sin

Hausawa su kan ce, da abokin daka a kan sha gari. A ganina, wannan karin magana ya bayyana yanayin huldar dake tsakanin Sin da Najeriya. Matukar an lura da hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen 2, to, za a rika ganin labarai masu kyau a kai a kai.

Za mu iya daukar wasu abubuwan da suka faru a kwanan nan a matsayin misali. Da farko dai, a karshen bara, babban bankin kasar Sin da babban bankin Nijeriya, sun sabunta yarjejeniyarsu ta musayar kudaden kasashensu da jimillarsu ta kai RMB yuan biliyan 15, ko kuma kudin Nijeriya kimanin Naira tiriliyan 3 da biliyan 280, inda aka samu wani sabon wa’adin yarjejeniyar na shekaru 3. Hakan zai fadada amfani da kudin kasa a cikin gida tsakanin Sin da Nijeriya, da saukaka harkokin cinikayya, da zuba jari, da hadin kai a fannin hada-hadar kudi tsakanin sassan biyu, da tinkarar kalubalen hawa da saukar darajar musayar kudi a kasuwannin kasa da kasa.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Majalisar Dokokin Legas Ta Tsige Kakakinta
  • Gwamnan Zamfara Ya Jajanta Wa Iyalan Da Harin Jirgin Sojoji Ya Rutsa Da Su

Na biyu shi ne, a kwanan baya, bankin CDB na kasar Sin ya samar da rance a zangon farko, wanda yawansa ya kai Euro miliyan 245, domin ci gaba da aikin gina layin dogo tsakanin jihohin Kaduna da Kano na arewacin Najeriya. Wani kamfanin kasar Sin ne ke daukar nauyin shimfida layin dogon da tsawonsa ya kai kilomita 203, wanda zai saukaka tafiye-tafiyen al’ummar arewacin Najeriya, bayan da aka kammala aikin ginin layin dogon.

ADVERTISEMENT

Na uku shi ne, karuwar cinikayyar da ake yi tsakanin Sin da Najeriya, ta sa wani kamfanin jigilar kayayyaki ta jiragen ruwa na kasa da kasa ya kaddamar da wani layin jigilar kaya kai tsaye tsakanin birnin Shanghai na Sin da Lagos na Najeriya, a farkon watan da muke ciki. Layin zai takaita lokacin jigilar kaya tsakanin biranen 2 zuwa kwanaki 27, kana farashin hidimar jigilar kayan ma ya ragu.

A sa’i daya kuma, manyan jami’an kasashen 2 suna cudanya da juna sosai. Misali, a kwanan baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya kammala ziyararsa a Najeriya. Sa’an nan a jiya, darekata janar mai kula da huldar abota tsakanin Najeriya da Sin, wadda ta shafi manyan tsare-tsare a dukkan fannoni na tarayyar Najeriya, Joseph Tegbe, shi ma ya isa birnin Beijing na Sin, inda ya fara wata ziyara a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Watakila za ka so ka san dalilin da ya sa ake samun cudanya sosai tsakanin Sin da Najeriya, kana huldar dake tsakaninsu na da kyau matuka?

Dalili na farko shi ne, kamar yadda ministan wajen kasar Najeriya, Yusuf Tuggar ya fada, yayin da yake ganawa da Mista Wang Yi a wannan karo, wato “Ba wani bambancin ra’ayi tsakanin Najeriya da Sin.” Hakika, kasashen Najeriya da Sin, bisa matsayinsu na manyan kasashe da tattalin arzikinsu ke kan hanyar ci gaba, suna da buri iri daya, wato zamanantar da kansu, da kyautata zaman rayuwar jama’a. Kana sam ba sa sha’awar ra’ayin kasashen yamma na ja-in-ja a fannin siyasa a duniya.

Ban da haka, Najeriya da Sin suna da moriya ta bai daya. Inda kasar Sin ke kokarin hada manufofin raya kasa da ta gabatar, da shirin raya tattalin arziki na Najeriya, don biyan bukatun Najeriya na samun ci gaba, da tabbatar da moriyar kamfanonin Sin a lokaci guda.

A nan gaba, yayin da ake kokarin gina yankin ciniki mai ‘yanci na nahiyar Afirka, Najeriya a bisa matsayinta na babbar kasa, da tattalin arziki mai karfi, tabbas za ta iya amfani da fifikonta a fannonin kayayyakin more rayuwa, da albarkatun kasa, da fasahohi, gami da jari, wajen jagorantar aikin cin gajiyar kasuwannin yankin da take ciki. Yayin da hadin gwiwar Sin da Najeriya zai iya taimakon Najeriya wajen taka muhimmiyar rawa a fannin raya yankin da take ciki, tare da haifar wa kamfanonin Sin masu zuba jari da riba. Tabbas wannan makoma mai haske, ita ce babban dalilin da ya sa ake samun dangantaka mai kyau tsakanin Najeriya da Sin. (Bello Wang)

Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin  Safarar Yara A Filato

Ƴansanda Sun Damƙe Fasto Bisa Laifin Safarar Yara A Filato

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.