• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya

by Leadership Hausa
3 years ago
in Labaran Kasuwanci
0
Nasarar Tsarin CBN Na Samar Da Kudaden Habaka Tattalin Arzikin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daukacin fadin duniya manyan Bankuna na bayar da gagarumar gudunmawa wajen habbaka wa da kuma bunkasa tattalin arzikin kasashe ta fannoni da dama.

A zahiri suna bayar gudunmawar ce saboda irin wadannan Bankunan nan ne makura wajen bayar da rancen kudade, kirkiro da tsare-tsaren kudade, musamman ganin cewa, irin wannan bankunan na a karkashin Gwamnati su ne ke tabbatar da samar da daitaito a tsare-tsaren hanyoyin da suka dace a tunkara don samar da canje-canjen sa suka kamata ga fannin tattalin arziki.

  • Asalin Abin Da Ya Sa Jama’a Ba Su Ganin Alfanun Tallafin Mai – Dakta Yakubu
  • ‘Yan Boko Haram Sun Kashe Masunta A Tafkin Chadi

Alal misali, a Nijeriya, dora Godwin Emefiele a matsayin Gwamnan Babban Bankin Nijeriya CBN za a iya cewa ya zuwa yanzu, kwaliiya ta biya kudin sabulu domin da hawarsa karagar shugabancin CBN ya kara inganta ayyukan Bankin, musamman ta hanyar inganta tsare-tsaren samar da kudade, inganta kasuwanin hada-hadar kudade da samar da hanya mai sauki don karbar kudade daga CBN don zuba jari a fannin kasuwanci ta hanyar samun rancen kudade daga CBN.

Daukin da Emefiele ya samar a bangaren harkokin Bankuna ya taimaka wa Gwamnatin matuka, ya na da kyau a sanar da cewa, koda yake irin wannan daukin na samar da kudade ba sabon abu ba ne domin an faro hakan ne tun a shekarar 1920.

Bugu da kari, akasarinManyan Bankuna da ke a kasashen da suka ci gaba suna samar da saukakar hanyoyi don bayar da goyon baya ga farfado da tattalin arzikinsu, inda alal misali, ko a shekarar 2008 zuwa 2009, irin wadannan kasashen sun taka muhimmiyar rasa wajen tsamo kasashen su daga matsayin tattalin arziki da da suka tsinci kansu a ciki da kuma a lokacin da duniya ta fuskanci kalubalen bullar annobar Korona, wanda samar da kudade na daga cikin dabarun da kasashen ke yi suna yi ne, don kara bunkasa tattalin arzikinsu.

Labarai Masu Nasaba

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da KuÉ—in Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

A bangaren Gwamnati mai ci a yanzu, ta samar da dauki na zuba sama da Naira Tiriliyan 3, inda wadannan kudaden suka taimaka wajen kara samar da ayyukan yi da kuma da kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan, inda hakan ya sa CBN tun a shekarar 2015, ya na ci gaba da kirkiro da shirye-shirye iriiri na samar da dauki yadda tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da tafiya yadda ake bukata.

Misalin, CBN ya kirkiro da tsarin (PPP) wanda za a mayar da hankali wajen karfafa kamfanonin cikin gida don ci gaba da sarrafa kaya a cikin kasar nan, wanda kuma hakan zai rage yawan shigo da kaya daga ketare da kara samar da aikin yi ga ‘yan Nijeriya da sauransu Har ila yau, a ranar 31 zuwa 28 na watan Janairun ne a babban bankin kasa CBN da ke Abuja aka kaddamar da mika Cakin Banki na jimllar Naira biliyan 23.2 ga bankunan kasuwanci bakwai da suka shiga cikin shirye-shiyen sa, inda su kuma wadannan Bankunan da suka amfana, za su yi amfani da wasu daga cikin kudaden wajen habbaka ayyukan su, samar da ayyukan yi a ‘yan kasar da sauransu.

Hakazalika, bisa wata kididdiga da aka samo daga CBN ta nuna cewa, CBN ya samar da daukin kudade ga fannin kerere da suka kai na jimllar Naira biliyan 803.36 inda tuni an zuba wadannan kudaden a cikin ayyuka 228 daban-daban da suka hada da Noma, Hakar Ma’adanai, inganta masana’antu da sauransu.

Haka kuma, CBN a watan Mayun 2020 ya gabatar da tsaretsaren wanzar da samar da dauki bayan bullar annobar Korona a kasar nan, wanda daya daga cikin manufar haka ita ce don a cike gibin da ake ganin bullar annobar za ta haifar ga fannoni daban-daban na tattalin arzikin Nijeriya da kuma masana’antu masu zaman kansu dake a kasar.

Kafin Godwin Emiefele ya samar da wannan daukin, fannin kere -kere na Nijeriya na samar da kasa da kashi 15 ne kacal ne a cikin dari, ga tattalin arzikin Nijeriya, inda hakan ya nuna babbar damuwar, ita ce yadda aka ci gaba da shigo da kaya daga ketare bayan alhali Nijeriya na da karfin da za ta iya sarrafa kaya har ta fitar zuwa ketare.

Har ila yau, tsarin da Emefiele ya kirkiro ya kara inganta dangantaka da Bankunan hada-hadar kudade na DMB da kuma a tsakanin sauran Cibiyoyin hada-hadar kudade inda daukacin su suka mayar da hankali a fannonin aikin noma, fannin kere-kere.

Bugu da kari, a karkashin samar da ainihin kayan aiki wato a Turance, (RSF), CBN ya zuba jimllar Naira tiriliyan 1.40 zuwa Naira tiriliyan 331, musamman domin amfani da kudaden a fannin aikin noma da fannin

ma’adanai da sauransu, inda kuma a daukin da CBN ya samar a shirin (RSSF), ya zuba Naira biliyan 166.21 don yin ayyyuka guda 25.

CBN ba wai ya mayar da hankali ne wajen samar da daukin kudade ba ne kawai, har da kuma wayar da kan masu bukatar zuba jari domin su zuba nasu jarin a fanoni don a kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

Har ila yau, a daukin da CBN a watan Afirilun 2022, ya samar biyo bayan bullar annobar Korona a kasar nan, ya dauki matakai da dama na fadada samar da dauki a fannin kiwon lafiya, inda CBN ya fitar da Naira biliyan 93 don a kara habaka fannin da kuma gudanar da ayyukan da ake sa burin cimma a kasar.

Manufar shirin shi ne, samar da bashi ga kamfanonin cikin gida da ke sarrafa magunguna, inda kuma tsarin ke bukatar ganin an kara samar da masu zaman kansu da ke son zuba jari a fannin kiwon lafiya, musamman don a rage yawan ‘yan Nijeriya da ke fita zuwa ketare neman lafiya.

Babban misali a nasarar da CBN ya samar a fannin na inganta kiwon lafiya a kasar shi ne, yadda a kwanan baya Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo yaje wani Asibitin da ke a cikin kasar nan don a duba lafiyarsa.

Wannan ya nuna a zahiri tsarin na Emefiele ya nuna akwai bukatar a kara wa bankunan kasuwanci na kasar kwarin gwiwa don su hadaka da masu son zuba jari a daukacin fannonin tattalin arzikin Nijeriya, kamar yadda Emefiele ke yawan yin kiraye-kiraye akai.

Akpan mazauni ne a garin Kalaba mai kuma yin fashin baki a kan tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Babban Bankin NijeriyaBankunaCBNEmefieleHabaka Tattalin ArzikiKasashe
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Masunta A Tafkin Chadi

Next Post

Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (I)

Related

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

4 months ago
Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da KuÉ—in Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024
Labarai

Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da KuÉ—in Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

5 months ago
Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri
Labarai

Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri

8 months ago
Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya
Labaran Kasuwanci

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

8 months ago
Rikicin Dangote Da NMDPRA: Gwamnatin Tarayya Zata Yi Sasanci
Labaran Kasuwanci

Rikicin Dangote Da NMDPRA: Gwamnatin Tarayya Zata Yi Sasanci

10 months ago
Tsarin ‘Yancin Kasuwanci A Afirka: Nijeriya Za Ta Amfana Da Dala Biliyan 50 
Labaran Kasuwanci

Tsarin ‘Yancin Kasuwanci A Afirka: Nijeriya Za Ta Amfana Da Dala Biliyan 50 

10 months ago
Next Post
Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (I)

Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (I)

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.