• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Mai Ciki Da Kudin Jabu Naira Miliyan 3.2

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
NDLEA Ta Cafke Mai Ciki Da Kudin Jabu Naira Miliyan 3.2
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi Ta Kasa NDLEA sun damke wata motar haya bas dauke da jabun kudi Naira miliyan 3.2 mallakar wasu mutum uku: Fabour Peter mai ciki wata takwas mai shekaru 24; Esther Adukwu, mai shekaru 27 da Ochigbo Michael, mai shekaru 39, wadanda aka kama a tashar mota ta Jabi da ke Abuja, a wani sumame da aka kai ranar Talata, 9 ga watan Afrilu, 2024, biyo bayan kama wasu kudaden na jabun Naira a Lokoja, jihar Kogi.

Hakan ta faru ne a daidai lokacin da jami’an NDLEA tare da hadin gwiwar rundunar sojojin ruwan Nijeriya da ke Lugard Base a Lokoja suka kama wani Aliyu Lawal dan shekara 37 a hanyar Lokoja zuwa Abuja ranar Litinin, tare da kwato dauri 620 na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 310 daga gare shi, yayin da jami’an NDLEA ta kama Jama Obodo, mai shekaru 44, da buhu 10 na wannan taba mai nauyin kilogiram 98 a kan titin Okene zuwa Lokoja-Abuja a cikin wata motar haya bas da ta taso daga Ilesha, jihar Osun ta hanyar zuwa Jihar Taraba a Afrilu.

  • Wata Kungiya Ta Shirya Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi 400,000 A Nijeriya
  • Jihar Benuwai Ta Bankado Mutum 35 Masu Yi Wa Sirin Tattara Harajinta Zagon-Kasa

A Jihar Kuros Riba, an kama wata bazawara mai shekaru 40 da haihuwa kuma mahaifiyar ‘ya’ya biyu, Misis Theodora a Bassey Edom, Calabar, sannan jami’an sun kama wata mata mai shekaru 40 da haihuwa a garin Bassey Edom da ke Calabar bisa laifin hadawa gami da sayar da wani sabon sinadari mai saurin kisa, NPS, a cikin gida. mai suna ‘Combine’, wato a hda gami da cakuda nau’ikan cannabis daban-daban da opioids wadanda aka jika a cikin danyen sinadarin Gin.

A lokacin da aka kama ta, an kwato lita 18 na sinadari mai hatsarin gaske a cikin bokitin  fenti.

Yayin dake amsa tambayoyi, ta yi ikirarin cewa ta fara samar da wadannan haramtattun magunguna ne da rarrabawa a watan Oktoban 2023. Wani wanda ake zargi, Godwin Okon Samuel, mai shekaru 48, an kama shi a unguwar Essit Ebum da ke Calabar da kilogiram 39.4 na tabar wiwi a ranar Talata, 9 ga Afrilu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Yayin da aka kama wasu mutum biyu: Sani Mohammed, mai shekaru 43, da Christopher Eze, mai shekaru 64 a unguwar Sabon Gari dake Kano a ranar Talata, 9 ga watan Afrilu, tare da kwato kwayoyi na opioid 900,000 daga hannunsu, jami’an NDLEA da ke sintiri a hanyar Owerri-Onitsha, Jihar Imo, a ranar Juma’a, 12 ga Afrilu, ta kama wata babbar motar daukar kaya mai lamba JGB 403DB, inda ta gano cannabis 230 na Satiba mai nauyin kilogiram 119 da aka boye a karkashin kayayyakin gida, bayan tsananta bincike.

 An kama akalla kilogiram 252 na tabar wiwi yayin wani samame da aka kai dajin Ijesa Isu, Jihar Ekiti a ranar Asabar 13 ga watan Afrilu yayin da wasu mutum hudu: Adamu Umar, mai shekaru 39; Abdullahi A Gimba, mai shekaru 27; da kuma Julius Uduakhomu, mai shekaru 28; an kama Micheal Sunday, mai shekaru 24, suna lodin kilogiram 40 na kaya maye a dakin da aka ajiye injin wata motar gas a kauyen Agho dake yankin Owan ta Gabas ta Jihar Edo.

An kuma gano babura biyu da aka yi amfani da su wajen kai kayan zuwa inda motar iskar gas din ta nufa.

A Jihar Ogun, an kama wani da ake zargi mai suna Ismaila Ogun a ranar Juma’a, 12 ga watan Afrilu da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 79 a Imeko, yayin da aka kama wani matashi mai suna Friday Abah mai shekaru 18 da kilogiram 410 na irin wannan taba a lokacin da jami’an NDLEA suka kai farmaki sansanin Obatedo, dajin Itaogbolu, a Karamar Hukumar Akure ta Arewa, Jihar Ondo.

 Wata sanarwa da Daraktan Yada labarai da bayar da shawarwari Femi Babafemi,ya fitar a shalkwatar hukumar ta NDLEA da ke Abuja, ya ce da irin wannan himma, tare da ba da umarni daban-daban na hukumar a fadin kasar nan, jami’an sun ci gaba da fafutukar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Wasu daga cikin ayukan sun hada da: Lakcar wayar da kan dalibai da ma’aikatan Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Gboko, a Gboko, Jihar Binuwai, wato WADA; Hafsoshin soji da mutum 15 na ‘Engineering Field Regiment Nigerian Army’, Topo, Badagry Lagos; mahautar nama ta Odo Eran, Osogbo, Jihar Osun kai ziyarar gami da ba da shawarwari ga Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, da dai sauransu.

Yayin da yake yaba wa Hafsoshi da jami’an Kogi, Cross Riber, Ondo, Ekiti, Ogun, Imo, Kano, da Edo na hukumar kwamandojin hukumar bisa bajintar da suka yi wajen rage yawan shan miyagun kwayoyi, Babban Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (Mai Ritaya), ya kuma yaba musu da takwarorinsu na dukkan bangarorin kasar nan kan yadda suka karfafa lakcocinsu na ‘WADA’, da nufin rage sha’awar shan miyagun kwayoyi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sauyin Yanayi: Dabarun Da  Za Su Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi

Next Post

An Lalata Haramtattun Rijyoyin Mai 7 Da Jiragen Ruwa 4 A Ribas

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

6 days ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

6 days ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

2 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Next Post
An Lalata Haramtattun Rijyoyin Mai 7 Da Jiragen Ruwa 4 A Ribas

An Lalata Haramtattun Rijyoyin Mai 7 Da Jiragen Ruwa 4 A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.