• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Masu Ta’ammali Da Ƙwayoyi 18,500 A 1 – Marwa

by Sadiq
5 months ago
in Manyan Labarai
0
NDLEA Ta Cafke Masu Ta’ammali Da Ƙwayoyi 18,500 A 1 – Marwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (Mai Ritaya), ya bayyana cewa hukumar ta cafke mutane sama da 18,500 da ake zargi da ta’ammuli da miyagun ƙwayoyi a bara.

Hakazalika, Marwa ya ce NDLEA ta ƙwace haramtattun ƙwayoyi masu nauyin kilogiram miliyan 2 da dubu 600 a shekarar.

  • Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta
  • Ana Kara Zuba Jarin Waje A Kasar Sin A Sabuwar Shekara

Ya yi wannan jawabi ne a lokacin da ake ƙaddamar da sabon ofishin hukumar da gwamnatin Amurka ta gina a Jihar Legas a ranar Talata.

Sabon ofishin, wanda za a riƙa amfani da shi wajen tattara da tantance hujjoji kan muggan ƙwayoyi, ya samu yabo daga Marwa, wanda ya gode wa gwamnatin Amurka saboda goyon bayan da ta ke bai wa NDLEA wajen yaƙi da safarar ƙwayoyi.

“Na gode wa Amurka bisa wannan ofishin da zai taimaka wajen tabbatar da shari’ar masu laifukan da suka shafi ƙwayoyi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

Ya ƙara da cewa duk da wannan nasarar, akwai sauran aiki a gaba domin kawo ƙarshen matsalar shaye-shaye da safarar ƙwayoyi a Nijeriya.

Marwa, ya bayyana cewa daga cikin waɗanda aka cafke a shekarar, an gurfanar da 3,250 a kotu, ciki har da gaggan masu safarar ƙwayoyi guda 10.

A gefe guda, ya ce hukumar ta yi nasarar sauya wa mutane sama da 8,200 tunani tare da raba su da shaye-shaye.

Marwa ya ce NDLEA za ta ci gaba da jajircewa wajen yaƙi da matsalar har sai ta rage yawan masu safarar ƙwayoyi da masu shan su a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ƘwayoyiMarwaNDLEA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Ba Da Umarnin Aiwatar Da Dukkanin Matakan Da Suka Wajaba Na Ceto Biyowa Bayan Girgizar Kasa A Xizang

Next Post

APC Na Mulkin Danniya A Nijeriya – Atiku

Related

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Manyan Labarai

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

4 hours ago
Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya
Manyan Labarai

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

5 hours ago
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
Manyan Labarai

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

17 hours ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur

22 hours ago
Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku
Manyan Labarai

Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku

24 hours ago
‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi
Manyan Labarai

Yadda ‘Yan Majalisa Ke Cusa Ayyuka Marasa Amfani A Kasafin Kuɗi – Rahoto

1 day ago
Next Post
Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba

APC Na Mulkin Danniya A Nijeriya – Atiku

LABARAI MASU NASABA

Goron Sallah

GORON JUMA’A

May 23, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

May 23, 2025
Ƴan Ta’adda 13,500 Aka Kashe Cikin Shekaru 2 – NSA Ribadu

Ƴan Ta’adda 13,500 Aka Kashe Cikin Shekaru 2 – NSA Ribadu

May 23, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

May 23, 2025
Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Yawa A Borno

Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Yawa A Borno

May 23, 2025
Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

May 23, 2025
Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

May 23, 2025
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

May 22, 2025
Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

May 22, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.