• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Saudiyya Sun Kulla Alakar Musayar Fasaha A Bangaren Mai

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Saudiyya

Gwamnatin Nijeriya da masarautar Saudiyya sun sanya hannun yarjejeniya domin bunkasa hadin guiwar fasaha, bangaren musayar fasahar sadarwa tsakanin kasashen biyu a bangaren mai da iskar gas.

Da ya ke bayani kan gagarumin matakin, a wata sanarwa, ministan albarkatun Mai, ya ce, hadin guiwar za ta taimaka wajen kara samar da hadin guiwa da fahimtar juna a tsakanin kasashen biyu dangane da bangaren samar da mai.

  • Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Ngaski Ya Samu ‘Yanci Bayan Shafe Makonni 3 A Hannun ‘Yan Bindiga
  • Za A Samar Wa ‘Yan Nijeriya Gida 80,000 Cikin Shekara 4

Sanarwar dauke da sanya hannun Nneamaka Okafor, kakakin ministan mai Heineken Lokpobiri, ya ce, ministan ya wakilci Nijeriya a wajen bikin sanya hannun, inda ministan makamashi na kasar Saudiyya ya wakilci sarki Abdulaziz bin Salman, yayin rattaba hannun.

Sanya hannun fahimtar junan (MoU), a cewar Lokpobiri, za ta taimaka sosai wa Nijeriya wajen kyautata fitar da mai da kuma fasaha hadi da bangaren makamashi.

Sanya hannun wacce ke da manufar kara kyautata alaka da juna da manufar samar da tsarin bunkasa harkokin mai da gas a kasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Babban manufar sanya hannun sun hada da taimaka wa juna wajen musayar bayanai, musayar raayin fasaha ta hanyar da za a samu kafa da aza yanayin fahimta da kasashen biyu za su amfani junansu, sanarwar ta kara.

Tare da Saudiyya za mu samu damar bunkasa fasahohi a bangaren hako mai da iskar gas, Nijeriya za ta samu tagomashi sosai da musayar ilimi.

Ta fuskacin musayar fasaha, Nijeriya za ta samu damar da za ta kyautata harkokin makamashi da zai taimaka sosai wajen kara bunkasa hanyoyin da ake bi wajen fitar da mai da kuma shiga tsarin duniya.

Kazalika, amincewar yarjejeniyar ana sa ran zai janyo hankalin masu zuba hannun jari kai tsaye da su zo Nijeriya domin zuba hannun jari a bangaren mai da iskar gas. Kasar Saudiyya da take taka gagarumin rawa a kasuwar makamashi na duniya, ta na da gagarumin rawar da za ta taka wajen ci gaban zuba jari a Nijeriya.

Wannan, zai taimaka matuka gaya wajen cigaban tattalin arziki, samar da ayyukan yi da kuma bunkasa shimfida ayyukan raya kasa. Kuma, wannan matakin zai taimaka sosai wajen kyautata kasuwancin mai a Nijeriya, sannan, bangarorin cigaban tattalin arziki da dama za su samu damar habaka, a cewar ministan.

Bugu da kari, tsarin fahimtar junan, zai kuma taimaka wajen kyautata hadin guiwar fasahohi da na harkokin kudi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit
Labarai

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Next Post
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025
An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.