• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Saudiyya Sun Kulla Alakar Musayar Fasaha A Bangaren Mai

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Nijeriya Da Saudiyya Sun Kulla Alakar Musayar Fasaha A Bangaren Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijeriya da masarautar Saudiyya sun sanya hannun yarjejeniya domin bunkasa hadin guiwar fasaha, bangaren musayar fasahar sadarwa tsakanin kasashen biyu a bangaren mai da iskar gas.

Da ya ke bayani kan gagarumin matakin, a wata sanarwa, ministan albarkatun Mai, ya ce, hadin guiwar za ta taimaka wajen kara samar da hadin guiwa da fahimtar juna a tsakanin kasashen biyu dangane da bangaren samar da mai.

  • Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Ngaski Ya Samu ‘Yanci Bayan Shafe Makonni 3 A Hannun ‘Yan Bindiga
  • Za A Samar Wa ‘Yan Nijeriya Gida 80,000 Cikin Shekara 4

Sanarwar dauke da sanya hannun Nneamaka Okafor, kakakin ministan mai Heineken Lokpobiri, ya ce, ministan ya wakilci Nijeriya a wajen bikin sanya hannun, inda ministan makamashi na kasar Saudiyya ya wakilci sarki Abdulaziz bin Salman, yayin rattaba hannun.

Sanya hannun fahimtar junan (MoU), a cewar Lokpobiri, za ta taimaka sosai wa Nijeriya wajen kyautata fitar da mai da kuma fasaha hadi da bangaren makamashi.

Sanya hannun wacce ke da manufar kara kyautata alaka da juna da manufar samar da tsarin bunkasa harkokin mai da gas a kasashen biyu.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Babban manufar sanya hannun sun hada da taimaka wa juna wajen musayar bayanai, musayar raayin fasaha ta hanyar da za a samu kafa da aza yanayin fahimta da kasashen biyu za su amfani junansu, sanarwar ta kara.

Tare da Saudiyya za mu samu damar bunkasa fasahohi a bangaren hako mai da iskar gas, Nijeriya za ta samu tagomashi sosai da musayar ilimi.

Ta fuskacin musayar fasaha, Nijeriya za ta samu damar da za ta kyautata harkokin makamashi da zai taimaka sosai wajen kara bunkasa hanyoyin da ake bi wajen fitar da mai da kuma shiga tsarin duniya.

Kazalika, amincewar yarjejeniyar ana sa ran zai janyo hankalin masu zuba hannun jari kai tsaye da su zo Nijeriya domin zuba hannun jari a bangaren mai da iskar gas. Kasar Saudiyya da take taka gagarumin rawa a kasuwar makamashi na duniya, ta na da gagarumin rawar da za ta taka wajen ci gaban zuba jari a Nijeriya.

Wannan, zai taimaka matuka gaya wajen cigaban tattalin arziki, samar da ayyukan yi da kuma bunkasa shimfida ayyukan raya kasa. Kuma, wannan matakin zai taimaka sosai wajen kyautata kasuwancin mai a Nijeriya, sannan, bangarorin cigaban tattalin arziki da dama za su samu damar habaka, a cewar ministan.

Bugu da kari, tsarin fahimtar junan, zai kuma taimaka wajen kyautata hadin guiwar fasahohi da na harkokin kudi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Harkar maiSaudiyyaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Kwato Wa Abba Hakkinsa A Kotun Koli – NNPP

Next Post

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

32 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

19 hours ago
Next Post
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.