• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Saudiyya Sun Kulla Alakar Musayar Fasaha A Bangaren Mai

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Nijeriya Da Saudiyya Sun Kulla Alakar Musayar Fasaha A Bangaren Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijeriya da masarautar Saudiyya sun sanya hannun yarjejeniya domin bunkasa hadin guiwar fasaha, bangaren musayar fasahar sadarwa tsakanin kasashen biyu a bangaren mai da iskar gas.

Da ya ke bayani kan gagarumin matakin, a wata sanarwa, ministan albarkatun Mai, ya ce, hadin guiwar za ta taimaka wajen kara samar da hadin guiwa da fahimtar juna a tsakanin kasashen biyu dangane da bangaren samar da mai.

  • Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Ngaski Ya Samu ‘Yanci Bayan Shafe Makonni 3 A Hannun ‘Yan Bindiga
  • Za A Samar Wa ‘Yan Nijeriya Gida 80,000 Cikin Shekara 4

Sanarwar dauke da sanya hannun Nneamaka Okafor, kakakin ministan mai Heineken Lokpobiri, ya ce, ministan ya wakilci Nijeriya a wajen bikin sanya hannun, inda ministan makamashi na kasar Saudiyya ya wakilci sarki Abdulaziz bin Salman, yayin rattaba hannun.

Sanya hannun fahimtar junan (MoU), a cewar Lokpobiri, za ta taimaka sosai wa Nijeriya wajen kyautata fitar da mai da kuma fasaha hadi da bangaren makamashi.

Sanya hannun wacce ke da manufar kara kyautata alaka da juna da manufar samar da tsarin bunkasa harkokin mai da gas a kasashen biyu.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Babban manufar sanya hannun sun hada da taimaka wa juna wajen musayar bayanai, musayar raayin fasaha ta hanyar da za a samu kafa da aza yanayin fahimta da kasashen biyu za su amfani junansu, sanarwar ta kara.

Tare da Saudiyya za mu samu damar bunkasa fasahohi a bangaren hako mai da iskar gas, Nijeriya za ta samu tagomashi sosai da musayar ilimi.

Ta fuskacin musayar fasaha, Nijeriya za ta samu damar da za ta kyautata harkokin makamashi da zai taimaka sosai wajen kara bunkasa hanyoyin da ake bi wajen fitar da mai da kuma shiga tsarin duniya.

Kazalika, amincewar yarjejeniyar ana sa ran zai janyo hankalin masu zuba hannun jari kai tsaye da su zo Nijeriya domin zuba hannun jari a bangaren mai da iskar gas. Kasar Saudiyya da take taka gagarumin rawa a kasuwar makamashi na duniya, ta na da gagarumin rawar da za ta taka wajen ci gaban zuba jari a Nijeriya.

Wannan, zai taimaka matuka gaya wajen cigaban tattalin arziki, samar da ayyukan yi da kuma bunkasa shimfida ayyukan raya kasa. Kuma, wannan matakin zai taimaka sosai wajen kyautata kasuwancin mai a Nijeriya, sannan, bangarorin cigaban tattalin arziki da dama za su samu damar habaka, a cewar ministan.

Bugu da kari, tsarin fahimtar junan, zai kuma taimaka wajen kyautata hadin guiwar fasahohi da na harkokin kudi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Harkar maiSaudiyyaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Kwato Wa Abba Hakkinsa A Kotun Koli – NNPP

Next Post

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Related

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

14 minutes ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

1 hour ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

1 hour ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

2 hours ago
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL
Manyan Labarai

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

4 hours ago
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

5 hours ago
Next Post
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.