• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
8 months ago
in Labarai
0
Ministan Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya ta gabatar da bukatarta na neman cikakken wakilci na didindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

Ta ce, ta bayar da gagarumin gudunmawa har sau akalla 41 a yayin gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya a fadin duniya, kuma ta tura dakarun ta sojin Nijeriya su sama da 200,000 a ayyukan Majalisar Dinkin Duniya, don haka ta ce, ta cancanci a ba ta kujerar dindindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

  • Jihar Kano Ta Musanta Zargin Karɓar Bashin Biliyan 177 Daga Faransa
  • An Kashe Jagororin ‘Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

Ministan tsaron Nijeriya, Mohammed Badaru, shi ne ya nuna wannan bukatar a yayin da yake jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79 da ya gudana a New York na Amurka ranar Lahadi.
“Nijeriya na kira ga yin garambawul ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ta yadda za a bai wa Afrika wakilci na dindindin domin shigo da kowani bangare cikin sha’anin wanzar da zaman lafiya da tsaro a fadin duniya.”

Badaru wanda ke magana a wajen taron tattauna yadda za a shigo da kowani bangare wajen kyautata zaman lafiya da tsaro a duniya. Ya ce muddin aka amince da bukatar nasu, za a kara samun wakilci wajen kyautata lamuran tsaro a Nahiyar Afirka.

Kwamitin tsaro dai na daga cikin muhimman bangarori 6 da suka hada Majalisar Dinkin Duniya. Yana da mambobin dindindin guda 15 da suke da alhakkin wanzar da zaman lafiya da tsaro a duniya, bayar da shawarar sabbin mambobin ga babban taron majalisar, amincewa da sauye-sauyen ga yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

An kafa kwamitin tsaron da nufin wanzar da ayyukan zaman lafiya da sanya takunkumi da kula da ayyukan sojoji.

A taron, ministan tsaron ya ce, “Nijeriya ta himmatu wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin duniya, tun lokacin da ta fara tura dakarunta na soji zuwa Congo a 1960, domin kwantar da tarzoma.
“Zuwa yau, Nijeriya ta ba da gudunmawarta wajen wanzar da zaman lafiya har sau 41 a ayyukan wanzar da zaman lafiya a fadin duniya, tare da amfani da sojoji sama da 200,000 a ayyukan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya.

“A ayyukan shiyya kuwa, Nijeriya ta taka rawa wajen gudanar da ayyukan wanzar da zaman lafiya a Cote d’Iboire, Guinea-Bissau, Gambia, Liberia, Mali, Sudan da Sierra Leone, da sauran kasashen, kuma ta bayar da gudunmawar kudade, kayan aiki, kwararrun soji, da hakan ya kaita ga zama kasa da ta fi kowace kasa bayar da gudunmawar soji da ‘yansanda a ayyukan Majalisar Dinkin Duniya.”

Shi kuma a nasa bangaren, ministan kula da harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar, ya yi kira ne ga shugabannin kasashen duniya da su bayar da kula wajen daurewar ci gaba, musamman a Nahiyar Afirka.
Tuggar ya bukaci kasashen da suka ci gaba da cika alkawuran da suka dauka na tallafa wa yankin Kudancin Duniya, yana mai jaddada cewa rashin cimma manufofin muradin karni ya kamata a tsawaita wa’adin shekarar 2030.

Ya kuma ba da shawarar sake yin kwaskwarima ga tsarin hada-hadar kudi na kasa da kasa domin tabbatar da gaskiya da rikon amana, tare da daukar kwararan matakai na yafe basussuka domin rage matsin tattalin arziki da kasashen Afirka ke fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

Next Post

Sama Da ‘Yan Nijeriya Miliyan 4 Suka Yi Zaman Kashe Wando A 2023 –NBS

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

6 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
NBS

Sama Da ‘Yan Nijeriya Miliyan 4 Suka Yi Zaman Kashe Wando A 2023 –NBS

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.