• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Ministan Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya ta gabatar da bukatarta na neman cikakken wakilci na didindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

Ta ce, ta bayar da gagarumin gudunmawa har sau akalla 41 a yayin gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya a fadin duniya, kuma ta tura dakarun ta sojin Nijeriya su sama da 200,000 a ayyukan Majalisar Dinkin Duniya, don haka ta ce, ta cancanci a ba ta kujerar dindindin a kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

  • Jihar Kano Ta Musanta Zargin Karɓar Bashin Biliyan 177 Daga Faransa
  • An Kashe Jagororin ‘Yan Bindiga, Sani Black Da Kachalla Makore A Zamfara

Ministan tsaron Nijeriya, Mohammed Badaru, shi ne ya nuna wannan bukatar a yayin da yake jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79 da ya gudana a New York na Amurka ranar Lahadi.
“Nijeriya na kira ga yin garambawul ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ta yadda za a bai wa Afrika wakilci na dindindin domin shigo da kowani bangare cikin sha’anin wanzar da zaman lafiya da tsaro a fadin duniya.”

Badaru wanda ke magana a wajen taron tattauna yadda za a shigo da kowani bangare wajen kyautata zaman lafiya da tsaro a duniya. Ya ce muddin aka amince da bukatar nasu, za a kara samun wakilci wajen kyautata lamuran tsaro a Nahiyar Afirka.

Kwamitin tsaro dai na daga cikin muhimman bangarori 6 da suka hada Majalisar Dinkin Duniya. Yana da mambobin dindindin guda 15 da suke da alhakkin wanzar da zaman lafiya da tsaro a duniya, bayar da shawarar sabbin mambobin ga babban taron majalisar, amincewa da sauye-sauyen ga yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

An kafa kwamitin tsaron da nufin wanzar da ayyukan zaman lafiya da sanya takunkumi da kula da ayyukan sojoji.

A taron, ministan tsaron ya ce, “Nijeriya ta himmatu wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin duniya, tun lokacin da ta fara tura dakarunta na soji zuwa Congo a 1960, domin kwantar da tarzoma.
“Zuwa yau, Nijeriya ta ba da gudunmawarta wajen wanzar da zaman lafiya har sau 41 a ayyukan wanzar da zaman lafiya a fadin duniya, tare da amfani da sojoji sama da 200,000 a ayyukan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya.

“A ayyukan shiyya kuwa, Nijeriya ta taka rawa wajen gudanar da ayyukan wanzar da zaman lafiya a Cote d’Iboire, Guinea-Bissau, Gambia, Liberia, Mali, Sudan da Sierra Leone, da sauran kasashen, kuma ta bayar da gudunmawar kudade, kayan aiki, kwararrun soji, da hakan ya kaita ga zama kasa da ta fi kowace kasa bayar da gudunmawar soji da ‘yansanda a ayyukan Majalisar Dinkin Duniya.”

Shi kuma a nasa bangaren, ministan kula da harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar, ya yi kira ne ga shugabannin kasashen duniya da su bayar da kula wajen daurewar ci gaba, musamman a Nahiyar Afirka.
Tuggar ya bukaci kasashen da suka ci gaba da cika alkawuran da suka dauka na tallafa wa yankin Kudancin Duniya, yana mai jaddada cewa rashin cimma manufofin muradin karni ya kamata a tsawaita wa’adin shekarar 2030.

Ya kuma ba da shawarar sake yin kwaskwarima ga tsarin hada-hadar kudi na kasa da kasa domin tabbatar da gaskiya da rikon amana, tare da daukar kwararan matakai na yafe basussuka domin rage matsin tattalin arziki da kasashen Afirka ke fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

Next Post

Sama Da ‘Yan Nijeriya Miliyan 4 Suka Yi Zaman Kashe Wando A 2023 –NBS

Related

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

3 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

3 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

5 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

6 hours ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

9 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

10 hours ago
Next Post
NBS

Sama Da ‘Yan Nijeriya Miliyan 4 Suka Yi Zaman Kashe Wando A 2023 –NBS

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.