• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Haɗa Gwiwa Da Amurka Wajen Inganta ‘Yancin ‘Yan Jarida

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Nijeriya Za Ta Haɗa Gwiwa Da Amurka Wajen Inganta ‘Yancin ‘Yan Jarida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana ƙudirin ma’aikatar sa na yin aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin ƙasar Amurka domin inganta ‘yancin manema labarai a Nijeriya.

Rabi’u Ibrahim, mai taimaka wa ministan kan harkokin yaɗa labarai, ya bayyana hakam a takardar da ya rattaba wa hannu cewa, Idris ya faɗi hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai jim kaɗan bayan ya yi wani zama da Jakadan Amurka a Nijeriya, Mista Richard Mills, a ofishin sa da ke Abuja a ranar Laraba.

  • Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Ministan ya ce: “Jakadan ya yi magana kan waɗansu abubuwa da yake ganin ya dace mu kula da su don inganta ‘yancin ‘yan jarida, mu kuma mun ba shi tabbaci kan irin abubuwan da muke yi, kuma ya ce, ya san cewa muna yin abin da ya dace wajen tabbatar da cewa, aikin jarida a Nijeriya ba kurum yana da cikakken ‘yanci ba ne, a’a har ma za a iya cewa yana daga cikin waɗanda suka fi ko’ina samun ‘yanci a faɗin duniya.

“Na san cewa, akwai wasu ‘yan matsaloli nan da can, kuma muna aiki don kulawa da irin waɗannan wuraren don dukkan mu mu ci moriyar abin da ake kira ‘yancin aikin jarida, wanda muhimmi ne a kowace ƙasa mai da’awar mulkin dimokuraɗiyya mai ƙarko.”

Ministan ya nanata yadda gwamnatin Tinubu ta ba ‘yancin ‘yan jarida muhimmanci kuma ya tabbatar da cewa, za ta ci gaba da inganta ‘yancin manema labarai a ƙasar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ya ce, sun kuma tattauna kan yadda za su haɗa kai su yi aiki tare wajen yaƙar baza labaran bogi da na ƙage a ƙasar.

Ya ce: “Ya yi magana kan labaran bogi da na ƙage da na ƙarya, duk waɗannan abubuwan mun tattauna kan su. Dukkan mu mun yi amanna da cewa babu yadda za a yi ka gina al’umma ingantacciya a yayin da kake yaɗa labaran ƙarya kuma ba ka ɗauki batun labaran bogi da na ƙage da gaske ba.”

A nasa jawabin, Jakada Mills ya ce zaman da suka yi da ministan sun yi shi ne domin su tattauna kan hanyoyin ƙarfafa dangantakar da ke akwai tsakanin gwamnatin Amurka da ma’aikatar, musamman abin da ya shafi ‘yancin ‘yan jarida da haƙƙoƙin manema labarai.

Ya yi la’akari da ƙoƙarin da ministan ke yi wajen haɓaka ‘yancin ‘yan jarida da haƙƙoƙin manema labarai a Nijeriya.

Jakaden na Amurka ya yi la’akari da babban ƙalubalen da matsalar baza labaran bogi ke janyowa, musamman ga ƙasashen da ke tafiyar da mulkin dimokiraɗiyya a faɗin duniya.

Ya ƙara da cewa sun kuma yi musayar ra’ayi da shawarwari kan yadda za a magance ƙalubalen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DimokuradiyyaNUJYan yancin jarida
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gabatar Da Y-20 A Bikin Baje Kolin Sararin Samaniya Da Tsaro Na Afirka

Next Post

Gandiroba Ya Hallaka Abokin Aikinsa Kan Abinci A Bauchi

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

2 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

2 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

10 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

10 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

13 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

13 hours ago
Next Post
Gandiroba Ya Hallaka Abokin Aikinsa Kan Abinci A Bauchi

Gandiroba Ya Hallaka Abokin Aikinsa Kan Abinci A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.