ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Haɗa Gwiwa Da Amurka Wajen Inganta ‘Yancin ‘Yan Jarida

by Sulaiman
2 years ago
Amurka

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana ƙudirin ma’aikatar sa na yin aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin ƙasar Amurka domin inganta ‘yancin manema labarai a Nijeriya.

Rabi’u Ibrahim, mai taimaka wa ministan kan harkokin yaɗa labarai, ya bayyana hakam a takardar da ya rattaba wa hannu cewa, Idris ya faɗi hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai jim kaɗan bayan ya yi wani zama da Jakadan Amurka a Nijeriya, Mista Richard Mills, a ofishin sa da ke Abuja a ranar Laraba.

  • Gwamnati Za Ta Gina Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa Sabbin Gidaje A Kano
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Ministan ya ce: “Jakadan ya yi magana kan waɗansu abubuwa da yake ganin ya dace mu kula da su don inganta ‘yancin ‘yan jarida, mu kuma mun ba shi tabbaci kan irin abubuwan da muke yi, kuma ya ce, ya san cewa muna yin abin da ya dace wajen tabbatar da cewa, aikin jarida a Nijeriya ba kurum yana da cikakken ‘yanci ba ne, a’a har ma za a iya cewa yana daga cikin waɗanda suka fi ko’ina samun ‘yanci a faɗin duniya.

ADVERTISEMENT

“Na san cewa, akwai wasu ‘yan matsaloli nan da can, kuma muna aiki don kulawa da irin waɗannan wuraren don dukkan mu mu ci moriyar abin da ake kira ‘yancin aikin jarida, wanda muhimmi ne a kowace ƙasa mai da’awar mulkin dimokuraɗiyya mai ƙarko.”

Ministan ya nanata yadda gwamnatin Tinubu ta ba ‘yancin ‘yan jarida muhimmanci kuma ya tabbatar da cewa, za ta ci gaba da inganta ‘yancin manema labarai a ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Ya ce, sun kuma tattauna kan yadda za su haɗa kai su yi aiki tare wajen yaƙar baza labaran bogi da na ƙage a ƙasar.

Ya ce: “Ya yi magana kan labaran bogi da na ƙage da na ƙarya, duk waɗannan abubuwan mun tattauna kan su. Dukkan mu mun yi amanna da cewa babu yadda za a yi ka gina al’umma ingantacciya a yayin da kake yaɗa labaran ƙarya kuma ba ka ɗauki batun labaran bogi da na ƙage da gaske ba.”

A nasa jawabin, Jakada Mills ya ce zaman da suka yi da ministan sun yi shi ne domin su tattauna kan hanyoyin ƙarfafa dangantakar da ke akwai tsakanin gwamnatin Amurka da ma’aikatar, musamman abin da ya shafi ‘yancin ‘yan jarida da haƙƙoƙin manema labarai.

Ya yi la’akari da ƙoƙarin da ministan ke yi wajen haɓaka ‘yancin ‘yan jarida da haƙƙoƙin manema labarai a Nijeriya.

Jakaden na Amurka ya yi la’akari da babban ƙalubalen da matsalar baza labaran bogi ke janyowa, musamman ga ƙasashen da ke tafiyar da mulkin dimokiraɗiyya a faɗin duniya.

Ya ƙara da cewa sun kuma yi musayar ra’ayi da shawarwari kan yadda za a magance ƙalubalen.

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Gandiroba Ya Hallaka Abokin Aikinsa Kan Abinci A Bauchi

Gandiroba Ya Hallaka Abokin Aikinsa Kan Abinci A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.