• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Bayelsa Ta Horas Da Jami’anta A Kan Kyautata Rayuwarsu

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Bayelsa Ta Horas Da Jami’anta A Kan Kyautata Rayuwarsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) Reshen Jihar Bayelsa ta horas da jami’anta a kan hanyoyin da za su inganta basirarsu musamman a kan hanyoyin kyautata rayuwarsu.

Hukumar, reshen jihar ta gayyato Kamfanin da ke bunƙasa ƙwazon ma’aikata, TINBIRD NIGERIA LIMITED domin ya horas da jami’an musamman kan abin da ta yi wa taken “Me ya kamata a yi bayan ritaya”.

  • NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

Horaswar ta fi mayar da hankali ce a kan yadda jami’an za su fahimci alfanun sana’o’i kamar noman rogo, kiwon zomo, kiwon dodon koɗi da sauran dabbobin da ake ci na rayuwa da aka fi amfani da su a Jihar Bayelsa.

An ƙarfafa gwiwar jami’an su riƙa gudanar da rayuwarsu daidai da abin da suke samu a matsayinsu na masu albashi, amma su ƙarfafa abokan aurensu su rungumi sana’o’i.

Ƙwararriyar mai horaswa a taron, wacce har ila yau ta gwanance wajen iya jawabi a bainar jama’a a Nijeriya da Amurka, Abigail Bokoyeibo, ta faɗakar da jami’an a kan muhimmancin kula da ƙa’idojin aiki da ririta wani abu daga cikin albashinsu tare da zuba jari a sana’o’in da za su kyautata yanayin rayuwarsu tun suna bakin aiki.

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Ta kuma nuna wa jami’an muhimmancin ƙarfafa iyalansu musamman waɗanda suke zaune ba su aikin komai, ta hanyar tsunduma su a sana’o’in gyaran gashi, aski, ado da kwalliya da ɗinki, sayar da ruwan burtsatse, sana’ar shige da ficen kuɗi ta POS baya ga noma da aka yarda wa kowane ma’aikacin gwamnati ya yi.

Daga cikin ƙwararrun da suka halarci horaswar har ila yau akwai Jami’ar Bunƙasa Kasuwanci ta Makarantar Tibird, Sarauniya Sese Ayoro, da Hon. Bibian George ta Cibiyar Bunƙasa Ci Gaban Mata da sauransu.

Da yake jawabi a taron horaswar, Kwanturolan NIS na Jihar Bayelsa, CI Sunday James ya nanata wa jami’an muhimmancin aiki tare da shawartarsu su ɗauki horaswar da muhimmanci tare da aiki da abin da aka horas da su a kai.

A cewar James, shekara 35 ta ritaya daga aiki kamar sanarwa ce ga duk ma’aikaci a kan ya shirya wa ritaya daga ranar da ya fara aiki.

Ya ba da misali da wani zancen hikima da masani Collins Powel ya yi a littafinsa mai sunan “Ranar Ritaya ta ƙarshe”, inda ya jaddada cewa ranar ritaya ta ƙarshe ita ce ranar tattara komatsai a yi sallama da kuma tafiya gida da abin da ka ririta lokacin da kake aiki, sai katin shaida.

Wakazalika, Kwanturolan ya ƙarfafa gwiwar jami’an hukumar su ɗauki ayyukansu da muhimmanci tare da kauce wa tserewa a bakin aiki ba tare da izini ba saboda gudun rasa aiki, domin ga masu neman aiki nan birjik suna gararamba a kan titi, don haka akwai buƙatar su ƙara riƙe abin da ke hannunsu da kyau.

Kwanturolan ya yi godiya ga Shugaban Hukumar ta NIS, muƙaddashin CGI Isah Idris Jere bisa ba su damar nuna ƙwarewarsu ta shugabanci a manyan ressan hukumar.

  • https://portal.immigration.gov.ng/

Horas da jami’an dai za ta ƙara musu ƙwazon aiki da kyautata jin daɗin rayuwarsu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Wajen Kasar Sin Ta Musanta Kalaman Amurka Da Birtaniya Game Da Yankin Hong Kong

Next Post

APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana’ar POS A Fadin Kasar Nan

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

8 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

11 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

12 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

13 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

15 hours ago
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
Labarai

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

15 hours ago
Next Post
APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana’ar POS A Fadin Kasar Nan

APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana'ar POS A Fadin Kasar Nan

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.