ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Bayelsa Ta Horas Da Jami’anta A Kan Kyautata Rayuwarsu

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Horas

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) Reshen Jihar Bayelsa ta horas da jami’anta a kan hanyoyin da za su inganta basirarsu musamman a kan hanyoyin kyautata rayuwarsu.

Hukumar, reshen jihar ta gayyato Kamfanin da ke bunƙasa ƙwazon ma’aikata, TINBIRD NIGERIA LIMITED domin ya horas da jami’an musamman kan abin da ta yi wa taken “Me ya kamata a yi bayan ritaya”.

  • NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

Horaswar ta fi mayar da hankali ce a kan yadda jami’an za su fahimci alfanun sana’o’i kamar noman rogo, kiwon zomo, kiwon dodon koɗi da sauran dabbobin da ake ci na rayuwa da aka fi amfani da su a Jihar Bayelsa.

ADVERTISEMENT

An ƙarfafa gwiwar jami’an su riƙa gudanar da rayuwarsu daidai da abin da suke samu a matsayinsu na masu albashi, amma su ƙarfafa abokan aurensu su rungumi sana’o’i.

Ƙwararriyar mai horaswa a taron, wacce har ila yau ta gwanance wajen iya jawabi a bainar jama’a a Nijeriya da Amurka, Abigail Bokoyeibo, ta faɗakar da jami’an a kan muhimmancin kula da ƙa’idojin aiki da ririta wani abu daga cikin albashinsu tare da zuba jari a sana’o’in da za su kyautata yanayin rayuwarsu tun suna bakin aiki.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

Ta kuma nuna wa jami’an muhimmancin ƙarfafa iyalansu musamman waɗanda suke zaune ba su aikin komai, ta hanyar tsunduma su a sana’o’in gyaran gashi, aski, ado da kwalliya da ɗinki, sayar da ruwan burtsatse, sana’ar shige da ficen kuɗi ta POS baya ga noma da aka yarda wa kowane ma’aikacin gwamnati ya yi.

Daga cikin ƙwararrun da suka halarci horaswar har ila yau akwai Jami’ar Bunƙasa Kasuwanci ta Makarantar Tibird, Sarauniya Sese Ayoro, da Hon. Bibian George ta Cibiyar Bunƙasa Ci Gaban Mata da sauransu.

Da yake jawabi a taron horaswar, Kwanturolan NIS na Jihar Bayelsa, CI Sunday James ya nanata wa jami’an muhimmancin aiki tare da shawartarsu su ɗauki horaswar da muhimmanci tare da aiki da abin da aka horas da su a kai.

A cewar James, shekara 35 ta ritaya daga aiki kamar sanarwa ce ga duk ma’aikaci a kan ya shirya wa ritaya daga ranar da ya fara aiki.

Ya ba da misali da wani zancen hikima da masani Collins Powel ya yi a littafinsa mai sunan “Ranar Ritaya ta ƙarshe”, inda ya jaddada cewa ranar ritaya ta ƙarshe ita ce ranar tattara komatsai a yi sallama da kuma tafiya gida da abin da ka ririta lokacin da kake aiki, sai katin shaida.

Wakazalika, Kwanturolan ya ƙarfafa gwiwar jami’an hukumar su ɗauki ayyukansu da muhimmanci tare da kauce wa tserewa a bakin aiki ba tare da izini ba saboda gudun rasa aiki, domin ga masu neman aiki nan birjik suna gararamba a kan titi, don haka akwai buƙatar su ƙara riƙe abin da ke hannunsu da kyau.

Kwanturolan ya yi godiya ga Shugaban Hukumar ta NIS, muƙaddashin CGI Isah Idris Jere bisa ba su damar nuna ƙwarewarsu ta shugabanci a manyan ressan hukumar.

  • https://portal.immigration.gov.ng/

Horas da jami’an dai za ta ƙara musu ƙwazon aiki da kyautata jin daɗin rayuwarsu.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Labarai

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Next Post
APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana’ar POS A Fadin Kasar Nan

APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana'ar POS A Fadin Kasar Nan

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.