• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Bayelsa Ta Horas Da Jami’anta A Kan Kyautata Rayuwarsu

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Horas

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) Reshen Jihar Bayelsa ta horas da jami’anta a kan hanyoyin da za su inganta basirarsu musamman a kan hanyoyin kyautata rayuwarsu.

Hukumar, reshen jihar ta gayyato Kamfanin da ke bunƙasa ƙwazon ma’aikata, TINBIRD NIGERIA LIMITED domin ya horas da jami’an musamman kan abin da ta yi wa taken “Me ya kamata a yi bayan ritaya”.

  • NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

Horaswar ta fi mayar da hankali ce a kan yadda jami’an za su fahimci alfanun sana’o’i kamar noman rogo, kiwon zomo, kiwon dodon koɗi da sauran dabbobin da ake ci na rayuwa da aka fi amfani da su a Jihar Bayelsa.

An ƙarfafa gwiwar jami’an su riƙa gudanar da rayuwarsu daidai da abin da suke samu a matsayinsu na masu albashi, amma su ƙarfafa abokan aurensu su rungumi sana’o’i.

Ƙwararriyar mai horaswa a taron, wacce har ila yau ta gwanance wajen iya jawabi a bainar jama’a a Nijeriya da Amurka, Abigail Bokoyeibo, ta faɗakar da jami’an a kan muhimmancin kula da ƙa’idojin aiki da ririta wani abu daga cikin albashinsu tare da zuba jari a sana’o’in da za su kyautata yanayin rayuwarsu tun suna bakin aiki.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Ta kuma nuna wa jami’an muhimmancin ƙarfafa iyalansu musamman waɗanda suke zaune ba su aikin komai, ta hanyar tsunduma su a sana’o’in gyaran gashi, aski, ado da kwalliya da ɗinki, sayar da ruwan burtsatse, sana’ar shige da ficen kuɗi ta POS baya ga noma da aka yarda wa kowane ma’aikacin gwamnati ya yi.

Daga cikin ƙwararrun da suka halarci horaswar har ila yau akwai Jami’ar Bunƙasa Kasuwanci ta Makarantar Tibird, Sarauniya Sese Ayoro, da Hon. Bibian George ta Cibiyar Bunƙasa Ci Gaban Mata da sauransu.

Da yake jawabi a taron horaswar, Kwanturolan NIS na Jihar Bayelsa, CI Sunday James ya nanata wa jami’an muhimmancin aiki tare da shawartarsu su ɗauki horaswar da muhimmanci tare da aiki da abin da aka horas da su a kai.

A cewar James, shekara 35 ta ritaya daga aiki kamar sanarwa ce ga duk ma’aikaci a kan ya shirya wa ritaya daga ranar da ya fara aiki.

Ya ba da misali da wani zancen hikima da masani Collins Powel ya yi a littafinsa mai sunan “Ranar Ritaya ta ƙarshe”, inda ya jaddada cewa ranar ritaya ta ƙarshe ita ce ranar tattara komatsai a yi sallama da kuma tafiya gida da abin da ka ririta lokacin da kake aiki, sai katin shaida.

Wakazalika, Kwanturolan ya ƙarfafa gwiwar jami’an hukumar su ɗauki ayyukansu da muhimmanci tare da kauce wa tserewa a bakin aiki ba tare da izini ba saboda gudun rasa aiki, domin ga masu neman aiki nan birjik suna gararamba a kan titi, don haka akwai buƙatar su ƙara riƙe abin da ke hannunsu da kyau.

Kwanturolan ya yi godiya ga Shugaban Hukumar ta NIS, muƙaddashin CGI Isah Idris Jere bisa ba su damar nuna ƙwarewarsu ta shugabanci a manyan ressan hukumar.

  • https://portal.immigration.gov.ng/

Horas da jami’an dai za ta ƙara musu ƙwazon aiki da kyautata jin daɗin rayuwarsu.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Next Post
APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana’ar POS A Fadin Kasar Nan

APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana'ar POS A Fadin Kasar Nan

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitul-mali Da Wakilin Cinikayyar Amurka

Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitul-mali Da Wakilin Cinikayyar Amurka

October 18, 2025
JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.