ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Bayelsa Ta Horas Da Jami’anta A Kan Kyautata Rayuwarsu

by Abdulrazaq Yahuza
4 years ago
Horas

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) Reshen Jihar Bayelsa ta horas da jami’anta a kan hanyoyin da za su inganta basirarsu musamman a kan hanyoyin kyautata rayuwarsu.

Hukumar, reshen jihar ta gayyato Kamfanin da ke bunƙasa ƙwazon ma’aikata, TINBIRD NIGERIA LIMITED domin ya horas da jami’an musamman kan abin da ta yi wa taken “Me ya kamata a yi bayan ritaya”.

  • NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

Horaswar ta fi mayar da hankali ce a kan yadda jami’an za su fahimci alfanun sana’o’i kamar noman rogo, kiwon zomo, kiwon dodon koɗi da sauran dabbobin da ake ci na rayuwa da aka fi amfani da su a Jihar Bayelsa.

ADVERTISEMENT

An ƙarfafa gwiwar jami’an su riƙa gudanar da rayuwarsu daidai da abin da suke samu a matsayinsu na masu albashi, amma su ƙarfafa abokan aurensu su rungumi sana’o’i.

Ƙwararriyar mai horaswa a taron, wacce har ila yau ta gwanance wajen iya jawabi a bainar jama’a a Nijeriya da Amurka, Abigail Bokoyeibo, ta faɗakar da jami’an a kan muhimmancin kula da ƙa’idojin aiki da ririta wani abu daga cikin albashinsu tare da zuba jari a sana’o’in da za su kyautata yanayin rayuwarsu tun suna bakin aiki.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Ta kuma nuna wa jami’an muhimmancin ƙarfafa iyalansu musamman waɗanda suke zaune ba su aikin komai, ta hanyar tsunduma su a sana’o’in gyaran gashi, aski, ado da kwalliya da ɗinki, sayar da ruwan burtsatse, sana’ar shige da ficen kuɗi ta POS baya ga noma da aka yarda wa kowane ma’aikacin gwamnati ya yi.

Daga cikin ƙwararrun da suka halarci horaswar har ila yau akwai Jami’ar Bunƙasa Kasuwanci ta Makarantar Tibird, Sarauniya Sese Ayoro, da Hon. Bibian George ta Cibiyar Bunƙasa Ci Gaban Mata da sauransu.

Da yake jawabi a taron horaswar, Kwanturolan NIS na Jihar Bayelsa, CI Sunday James ya nanata wa jami’an muhimmancin aiki tare da shawartarsu su ɗauki horaswar da muhimmanci tare da aiki da abin da aka horas da su a kai.

A cewar James, shekara 35 ta ritaya daga aiki kamar sanarwa ce ga duk ma’aikaci a kan ya shirya wa ritaya daga ranar da ya fara aiki.

Ya ba da misali da wani zancen hikima da masani Collins Powel ya yi a littafinsa mai sunan “Ranar Ritaya ta ƙarshe”, inda ya jaddada cewa ranar ritaya ta ƙarshe ita ce ranar tattara komatsai a yi sallama da kuma tafiya gida da abin da ka ririta lokacin da kake aiki, sai katin shaida.

Wakazalika, Kwanturolan ya ƙarfafa gwiwar jami’an hukumar su ɗauki ayyukansu da muhimmanci tare da kauce wa tserewa a bakin aiki ba tare da izini ba saboda gudun rasa aiki, domin ga masu neman aiki nan birjik suna gararamba a kan titi, don haka akwai buƙatar su ƙara riƙe abin da ke hannunsu da kyau.

Kwanturolan ya yi godiya ga Shugaban Hukumar ta NIS, muƙaddashin CGI Isah Idris Jere bisa ba su damar nuna ƙwarewarsu ta shugabanci a manyan ressan hukumar.

  • https://portal.immigration.gov.ng/

Horas da jami’an dai za ta ƙara musu ƙwazon aiki da kyautata jin daɗin rayuwarsu.

 

Horas
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana’ar POS A Fadin Kasar Nan

APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana'ar POS A Fadin Kasar Nan

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.