• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Rahotonni
0
NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), CGI Isah Jere Idris, ya amince da sauya wuraren aiki ga manyan jami’ai 69 zuwa manyan ofisoshin hukumar na shiyyoyi da jihohi da ke sassan kasar nan.

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulda da jama’a na hukumar, ACI Amos Okpu ta bayyana cewa daga cikin adadin jami’an da aka sauya wa wuraren aikin akwai masu mukaman Kananan Mataimakan Kwanturola Janar (ACG) guda takwas sai masu mukaman Kwanturololi (CIS) guda 61 da aka rarraba su a sassan manyan ofisoshin hukumar.

  • Hukumar Kwastom Ta Cafke Miyagun Kwayoyi Na Kimanin Biliyan N1.4 A Legas
  • Hukumar NDLEA Ta Kona 560,068kg Na Hodar Iblis Da Wasu Kwayoyi A Legas

Cikin masu mukaman ACG da aka sauya wa wuraren aikin akwai ACG KM Amao wanda a da yake Kwanturolan Jihar Ogun amma yanzu an maida shi Sashen Ayyuka Na Gaba Daya a shalkwatar hukumar da ke Abuja, sa’ilin da ACG KN Nandap wanda a baya yake kula da Babban Filin Jiragen Sama na Murtala Mohammed da ke Legas a yanzu kuma aka sauya masa zuwa Sashen Bayar da Takardu ga Bakin Waje (CERPAC) a shalkwata.

Har ila yau, ACG Abdullahi M Usman a yanzu shi ne Shugaban Sashen Kula da Shige da Fice na Yau da Kullum a shalkwatar hukumar, yayin da ACG BN Alawode ya zama Shugaban Sashen Kula da Walwala da Daidaiton Jinsi, sai kuma ACG EC Esedo da aka mayar zuwa Ofishin Shiyya ta hudu da ke Minna.

Shi kuwa ACG MA Ushie na Sashen Yaki da Damfara an mayar da shi zuwa Sashen Difilomasiyya da Fasfo, sai ACG ES Fagbamigba wanda a da yake kula da Babban ofishin Iyaka na Idi-Iroko da aka tura ya zama shugaban kula da iyakokin kasa na kan-tudu a shalkwata.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Daga cikin masu mukaman Kwanturololi da aka sauya wa wuraren aikin kuwa akwai Compt. AO Adesokan da aka mayar zuwa Babban Filin Jiragen Sama na Murtala Mohammed da ke Legas daga Sashen Horaswa da Inganta Kwazon Ma’aikata, yayin da mukaddashin babban jami’in ofoshin Kwanturola Janar, Compt. Ahmed Mustapha ya zama sabon Kwanturolan Kano.

Sauran sun hada da Compt. Shittu Olajire Fatai wanda a yanzu aka mayar da shi Ofishin Kula da Iyaka na Legas; da Compt. Gwama Muhammad wanda a yanzu shi aka ba shugabancin Ofishin kula da iyaka na Idi-Iroko; da Compt. MM Saddik wanda a yanzu aka ba shi matsayin Babban Jami’in Ofishin Kwanturola Janar.

Shi kuwa Compt. AO Bewaji an mayar da shi ne zuwa shalkwatar hukumar yayin da Compt. Michael Dike ya karbi ragama a matsayin Kwanturolan Iyaka na Seme da ke Legas. Shi kuwa Kwanturola mai kula da da’ar aiki an tura shi ya shugabanci yankin Jihar Osun yayin da Compt.

Sabo A Rano da ya kasance Kwamandan Makarantar Horas da Jami’ai ta Kano aka mayar da shi zuwa Jihar Gombe.

Bugu da kari, Compt. FD Dakat na Sashen kula da tasoshin ruwa aka mayar da shi zuwa Jihar Akwa Ibom inda zai karbi ragama daga Compt. GE Didel wanda aka mayar zuwa sashen shige da fice a shalkwata, da dai sauransu.

Shugaban Hukumar ta NIS, Isah Jere ya hori dukkan jami’an da aka sauya wa wuraren aikin su yi amfani da basirar da Allah ya yi musu a wuraren da aka tura su wajen inganta aiki da tsaron kasa. Sauyin aikin dai ya fara aiki ne nan take.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 69AbujaJami'aikanoLegasNISSauya Wurin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Sufeton ‘Yansanda Tafa Balogun

Next Post

Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

1 day ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

5 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

6 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

1 week ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

LABARAI MASU NASABA

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.