ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

by Abdulrazaq Yahuza
4 years ago
NNPC

A makon jiya ne, bayan cika shekara 44 da kafuwa aka sauya fasalin kamfanin albarkatun mai na NNPC zuwa cikakken kamfani mai zaman kansa. Ana fatan wannan tsarin zai kai ga gwamnatin tarayya ta tsame hannunta daga zuba kudi wajen tafiyar da harkokin kamfanin kamar yadda dokar kafa kamfanin ta samar a shekarar 1977.

Sabon kamfanin NNPC Ltd zai gudanar da ayyukansa ne a halin yanzu kamar yadda dokokin kafa kamfanonin Nijeriya ta samar a karkashin dokar ‘Company and Allied Matters Act (CAMA)’.

  • Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya
  • Hukumar Kwastom Ta Cafke Miyagun Kwayoyi Na Kimanin Biliyan N1.4 A Legas

A wannan tsarin, Ma’aikatar Albarkatun Mai da Ma’aikatar Kudi suke da mallakin jarin kamfanin gaba daya ana kuma sa ran a nan gaba za a bude hannun jarin kamfanin ga al’ummar kasar ta hanyar sayar da hannayen jarin.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa a ranar 16 ga watan Agusta 2021 ne Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sanya hannun a kan dokar alkinta albarkatun man fetur wanda ya samar da tabbatar da cefanar da kamfanin NNPC don ya zama kamfani mai zaman kanshi, ana sa ran kamfanin zai gudanar da ayyukansa ta hanyar neman riba ba tare da dogara da kudaden gwamnati ba, ana kuma bukatar ganin ribar da kamfanin ke samarwa ta amfanar da masu hannun jari, wanda daga nan ne kuma za a shirya ganin hannun jarin gwamnati ya zama kashi 20 a cikin dari sauran kuma ga al’umm.

Da wannan shirin da aka samar, za a cigaba da gudanar da NNPC ne kamar yadda ake tafiyar da takwarorionta a sassan duniya, kamar Aramco a kasar Saudi Arabia, Petronas a Malaysia da Petrobras na kasar Brazil.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

A shekarar 2020, Aramco ta zama daya daga cikin manyan kamfanoni a duniya inda a ranar 11 ga watan Mayu kudin ribar da ta samu ya zarce na kamfanoni irin su Apple Inc. a na kuma fatan cewa, a ‘yan shekaru masu zuwa kamfanin NNPC zai zama kamar Aramco a wajen samar da kudaden shiga ga kasar nan.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, tabbas wannan mataki ne da ya dace, muna kuma fatan za a samu nasara irin yadda muka gani tattare da kamfanin samar da iskar gas ta NLNG inda ta samar da ribar Dala Biliyan 100 a matsayin kudin shiga a shekara, muna da tabbacin cewa, in har aka sake wa sabon NNPC mara zai iya samun irin wannan nasarar.

Yana da matukar muhimmanci a bar sabon kamfanin NNPC ya gudanar da harkokinsa ba tare da katsalandan ba don samun cikakiyar nasarar da ake bukata.

Ana sa ran kamfanin NNPC ya zamab abban kamfani nan da shekaru masu zuwa, mun yi imanin za ta iya zama cikin manyan kamfanonin da za a yi alfahari da su a duniya.

Yana kuma da matukarm uhimmnanci a ra’ayinmu, sabbin mahukuntan NNPC su gudanar da cikakken bincike tare da garanbawul ga ma’aikatan kamfanin.

Wannan na da muhimanci don toshe duk wata hanyar da ake barnar kudaden kasa wannan abin da aka yi ta zargin kamfanin ke nan a baya. Ya kamata sabin masu tafiyar da kamfanin su tabbatar da babu almundahana da cin hanci da rashawa tattare da tafiyar.

Ya kuma kamata a dauki kwararrun ‘yan Nijeriya daga kamfanonin mai na duniya don samar da canjin da ake bukata.

Babbar tambaya anan ita ce ya za a yi da tallafin mai wanda yake tatse dan tattalin arzikin kasar nan da yake a kan gargara. Gwamnatin tarayya ta kiyasta kashe Naira Tiriliyan 6.72 a kan tallafin man fetur a shekara mai zuwa wannan kudin da aka kiyasata ya zarce kudin da aka kashe a wannan shekarar na Naira Tiriliyan 2.53.

A ra’ayinmu wannan ba abin da za a amince da shi ba ne.

Masana sun yi imanin cewa, da wannan cefanar da NNPC da aka yi ba za ta rika zuba kudade a asusun gwamnatin tarayya ba, wanda hakan na nufin cewa, a yanzu babu kudaden da gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi za su rinkarabawa a tsakaninsu, amma tabbas za ta rika biyan dukkan hakoki na haraji da sauransu ga gwamnati.

A ra’ayinmu, wannan labari ne, mai kyau don zai tilastawa yawancin gwamnonin jihohi neman wasu hanyoyin samar da kudaden gudanar da harkokinsu ba tare da jiran kudi daga gwamnatin tarayya ba.

Mun dade muna kira a wannan shafin cewa, ya kamata gwamnoni su zama kamar shugabanin manyan kamfanoni ta hanyar nema wa jihohinsu kudaden shiga. Amma yanzu da a aka samu janyewar wadannan kudaden ya zama dole su nema kansu wasu hanyoyi na daban na neman kudaden shiga.

Abin takaici kuma shi ne a halin yanzu da ya kamata Nijeriya ta ribaci yadda farashin man fetur ke hauhawa a kasuwannin duniya sakamakon yakin Rasha da Yukiren amma abin ba haka yake ba, a kan haka muke kira ga sabbin mahukuntan NNPC su duba yadda Nijeriya za ta ci gajiyar irin wannan lamarin don amfanin al’umma.

Muna kara jinjina ga gwamnatin tarayya a kan wannan mataki da ta dauka.

NNPC
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sako Wasu Mutum 2 Da Suka Sace A Wata Cocin Jihar Abiya 

DA DUMI-DUMI: 'Yan Bindiga Sun Sace Wani Basaraken Gargajiya Da Wasu Mutum 3 A Ondo

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.