ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

by Abdulrazaq Yahuza
4 years ago
NNPC

A makon jiya ne, bayan cika shekara 44 da kafuwa aka sauya fasalin kamfanin albarkatun mai na NNPC zuwa cikakken kamfani mai zaman kansa. Ana fatan wannan tsarin zai kai ga gwamnatin tarayya ta tsame hannunta daga zuba kudi wajen tafiyar da harkokin kamfanin kamar yadda dokar kafa kamfanin ta samar a shekarar 1977.

Sabon kamfanin NNPC Ltd zai gudanar da ayyukansa ne a halin yanzu kamar yadda dokokin kafa kamfanonin Nijeriya ta samar a karkashin dokar ‘Company and Allied Matters Act (CAMA)’.

  • Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya
  • Hukumar Kwastom Ta Cafke Miyagun Kwayoyi Na Kimanin Biliyan N1.4 A Legas

A wannan tsarin, Ma’aikatar Albarkatun Mai da Ma’aikatar Kudi suke da mallakin jarin kamfanin gaba daya ana kuma sa ran a nan gaba za a bude hannun jarin kamfanin ga al’ummar kasar ta hanyar sayar da hannayen jarin.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa a ranar 16 ga watan Agusta 2021 ne Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sanya hannun a kan dokar alkinta albarkatun man fetur wanda ya samar da tabbatar da cefanar da kamfanin NNPC don ya zama kamfani mai zaman kanshi, ana sa ran kamfanin zai gudanar da ayyukansa ta hanyar neman riba ba tare da dogara da kudaden gwamnati ba, ana kuma bukatar ganin ribar da kamfanin ke samarwa ta amfanar da masu hannun jari, wanda daga nan ne kuma za a shirya ganin hannun jarin gwamnati ya zama kashi 20 a cikin dari sauran kuma ga al’umm.

Da wannan shirin da aka samar, za a cigaba da gudanar da NNPC ne kamar yadda ake tafiyar da takwarorionta a sassan duniya, kamar Aramco a kasar Saudi Arabia, Petronas a Malaysia da Petrobras na kasar Brazil.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

A shekarar 2020, Aramco ta zama daya daga cikin manyan kamfanoni a duniya inda a ranar 11 ga watan Mayu kudin ribar da ta samu ya zarce na kamfanoni irin su Apple Inc. a na kuma fatan cewa, a ‘yan shekaru masu zuwa kamfanin NNPC zai zama kamar Aramco a wajen samar da kudaden shiga ga kasar nan.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, tabbas wannan mataki ne da ya dace, muna kuma fatan za a samu nasara irin yadda muka gani tattare da kamfanin samar da iskar gas ta NLNG inda ta samar da ribar Dala Biliyan 100 a matsayin kudin shiga a shekara, muna da tabbacin cewa, in har aka sake wa sabon NNPC mara zai iya samun irin wannan nasarar.

Yana da matukar muhimmanci a bar sabon kamfanin NNPC ya gudanar da harkokinsa ba tare da katsalandan ba don samun cikakiyar nasarar da ake bukata.

Ana sa ran kamfanin NNPC ya zamab abban kamfani nan da shekaru masu zuwa, mun yi imanin za ta iya zama cikin manyan kamfanonin da za a yi alfahari da su a duniya.

Yana kuma da matukarm uhimmnanci a ra’ayinmu, sabbin mahukuntan NNPC su gudanar da cikakken bincike tare da garanbawul ga ma’aikatan kamfanin.

Wannan na da muhimanci don toshe duk wata hanyar da ake barnar kudaden kasa wannan abin da aka yi ta zargin kamfanin ke nan a baya. Ya kamata sabin masu tafiyar da kamfanin su tabbatar da babu almundahana da cin hanci da rashawa tattare da tafiyar.

Ya kuma kamata a dauki kwararrun ‘yan Nijeriya daga kamfanonin mai na duniya don samar da canjin da ake bukata.

Babbar tambaya anan ita ce ya za a yi da tallafin mai wanda yake tatse dan tattalin arzikin kasar nan da yake a kan gargara. Gwamnatin tarayya ta kiyasta kashe Naira Tiriliyan 6.72 a kan tallafin man fetur a shekara mai zuwa wannan kudin da aka kiyasata ya zarce kudin da aka kashe a wannan shekarar na Naira Tiriliyan 2.53.

A ra’ayinmu wannan ba abin da za a amince da shi ba ne.

Masana sun yi imanin cewa, da wannan cefanar da NNPC da aka yi ba za ta rika zuba kudade a asusun gwamnatin tarayya ba, wanda hakan na nufin cewa, a yanzu babu kudaden da gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi za su rinkarabawa a tsakaninsu, amma tabbas za ta rika biyan dukkan hakoki na haraji da sauransu ga gwamnati.

A ra’ayinmu, wannan labari ne, mai kyau don zai tilastawa yawancin gwamnonin jihohi neman wasu hanyoyin samar da kudaden gudanar da harkokinsu ba tare da jiran kudi daga gwamnatin tarayya ba.

Mun dade muna kira a wannan shafin cewa, ya kamata gwamnoni su zama kamar shugabanin manyan kamfanoni ta hanyar nema wa jihohinsu kudaden shiga. Amma yanzu da a aka samu janyewar wadannan kudaden ya zama dole su nema kansu wasu hanyoyi na daban na neman kudaden shiga.

Abin takaici kuma shi ne a halin yanzu da ya kamata Nijeriya ta ribaci yadda farashin man fetur ke hauhawa a kasuwannin duniya sakamakon yakin Rasha da Yukiren amma abin ba haka yake ba, a kan haka muke kira ga sabbin mahukuntan NNPC su duba yadda Nijeriya za ta ci gajiyar irin wannan lamarin don amfanin al’umma.

Muna kara jinjina ga gwamnatin tarayya a kan wannan mataki da ta dauka.

NNPC
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

NNPC
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
NNPC
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sako Wasu Mutum 2 Da Suka Sace A Wata Cocin Jihar Abiya 

DA DUMI-DUMI: 'Yan Bindiga Sun Sace Wani Basaraken Gargajiya Da Wasu Mutum 3 A Ondo

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.