• Leadership Hausa
Saturday, June 3, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya

by Abdulrazaq Yahuza
10 months ago
in Rahotonni
0
Bukatar Tabbatar Da Sabon Kamfanin NNPC Ya Ba Mara da Kunya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon jiya ne, bayan cika shekara 44 da kafuwa aka sauya fasalin kamfanin albarkatun mai na NNPC zuwa cikakken kamfani mai zaman kansa. Ana fatan wannan tsarin zai kai ga gwamnatin tarayya ta tsame hannunta daga zuba kudi wajen tafiyar da harkokin kamfanin kamar yadda dokar kafa kamfanin ta samar a shekarar 1977.

Sabon kamfanin NNPC Ltd zai gudanar da ayyukansa ne a halin yanzu kamar yadda dokokin kafa kamfanonin Nijeriya ta samar a karkashin dokar ‘Company and Allied Matters Act (CAMA)’.

  • Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya
  • Hukumar Kwastom Ta Cafke Miyagun Kwayoyi Na Kimanin Biliyan N1.4 A Legas

A wannan tsarin, Ma’aikatar Albarkatun Mai da Ma’aikatar Kudi suke da mallakin jarin kamfanin gaba daya ana kuma sa ran a nan gaba za a bude hannun jarin kamfanin ga al’ummar kasar ta hanyar sayar da hannayen jarin.

Idan za a iya tunawa a ranar 16 ga watan Agusta 2021 ne Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sanya hannun a kan dokar alkinta albarkatun man fetur wanda ya samar da tabbatar da cefanar da kamfanin NNPC don ya zama kamfani mai zaman kanshi, ana sa ran kamfanin zai gudanar da ayyukansa ta hanyar neman riba ba tare da dogara da kudaden gwamnati ba, ana kuma bukatar ganin ribar da kamfanin ke samarwa ta amfanar da masu hannun jari, wanda daga nan ne kuma za a shirya ganin hannun jarin gwamnati ya zama kashi 20 a cikin dari sauran kuma ga al’umm.

Da wannan shirin da aka samar, za a cigaba da gudanar da NNPC ne kamar yadda ake tafiyar da takwarorionta a sassan duniya, kamar Aramco a kasar Saudi Arabia, Petronas a Malaysia da Petrobras na kasar Brazil.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya

A shekarar 2020, Aramco ta zama daya daga cikin manyan kamfanoni a duniya inda a ranar 11 ga watan Mayu kudin ribar da ta samu ya zarce na kamfanoni irin su Apple Inc. a na kuma fatan cewa, a ‘yan shekaru masu zuwa kamfanin NNPC zai zama kamar Aramco a wajen samar da kudaden shiga ga kasar nan.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, tabbas wannan mataki ne da ya dace, muna kuma fatan za a samu nasara irin yadda muka gani tattare da kamfanin samar da iskar gas ta NLNG inda ta samar da ribar Dala Biliyan 100 a matsayin kudin shiga a shekara, muna da tabbacin cewa, in har aka sake wa sabon NNPC mara zai iya samun irin wannan nasarar.

Yana da matukar muhimmanci a bar sabon kamfanin NNPC ya gudanar da harkokinsa ba tare da katsalandan ba don samun cikakiyar nasarar da ake bukata.

Ana sa ran kamfanin NNPC ya zamab abban kamfani nan da shekaru masu zuwa, mun yi imanin za ta iya zama cikin manyan kamfanonin da za a yi alfahari da su a duniya.

Yana kuma da matukarm uhimmnanci a ra’ayinmu, sabbin mahukuntan NNPC su gudanar da cikakken bincike tare da garanbawul ga ma’aikatan kamfanin.

Wannan na da muhimanci don toshe duk wata hanyar da ake barnar kudaden kasa wannan abin da aka yi ta zargin kamfanin ke nan a baya. Ya kamata sabin masu tafiyar da kamfanin su tabbatar da babu almundahana da cin hanci da rashawa tattare da tafiyar.

Ya kuma kamata a dauki kwararrun ‘yan Nijeriya daga kamfanonin mai na duniya don samar da canjin da ake bukata.

Babbar tambaya anan ita ce ya za a yi da tallafin mai wanda yake tatse dan tattalin arzikin kasar nan da yake a kan gargara. Gwamnatin tarayya ta kiyasta kashe Naira Tiriliyan 6.72 a kan tallafin man fetur a shekara mai zuwa wannan kudin da aka kiyasata ya zarce kudin da aka kashe a wannan shekarar na Naira Tiriliyan 2.53.

A ra’ayinmu wannan ba abin da za a amince da shi ba ne.

Masana sun yi imanin cewa, da wannan cefanar da NNPC da aka yi ba za ta rika zuba kudade a asusun gwamnatin tarayya ba, wanda hakan na nufin cewa, a yanzu babu kudaden da gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi za su rinkarabawa a tsakaninsu, amma tabbas za ta rika biyan dukkan hakoki na haraji da sauransu ga gwamnati.

A ra’ayinmu, wannan labari ne, mai kyau don zai tilastawa yawancin gwamnonin jihohi neman wasu hanyoyin samar da kudaden gudanar da harkokinsu ba tare da jiran kudi daga gwamnatin tarayya ba.

Mun dade muna kira a wannan shafin cewa, ya kamata gwamnoni su zama kamar shugabanin manyan kamfanoni ta hanyar nema wa jihohinsu kudaden shiga. Amma yanzu da a aka samu janyewar wadannan kudaden ya zama dole su nema kansu wasu hanyoyi na daban na neman kudaden shiga.

Abin takaici kuma shi ne a halin yanzu da ya kamata Nijeriya ta ribaci yadda farashin man fetur ke hauhawa a kasuwannin duniya sakamakon yakin Rasha da Yukiren amma abin ba haka yake ba, a kan haka muke kira ga sabbin mahukuntan NNPC su duba yadda Nijeriya za ta ci gajiyar irin wannan lamarin don amfanin al’umma.

Muna kara jinjina ga gwamnatin tarayya a kan wannan mataki da ta dauka.

Tags: BuhariKamfanin Mai Fetur Na KasaMele KyariNNPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Sauya Wuraren Aiki Ga Manyan Jami’ai 69

Next Post

DA DUMI-DUMI: ‘Yan Bindiga Sun Sace Wani Basaraken Gargajiya Da Wasu Mutum 3 A Ondo

Related

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga
Rahotonni

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

22 mins ago
Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya
Rahotonni

Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya

20 hours ago
Yadda Amurka Ta Yi Kokarin Amfani Da Nukiliya Wajen Tarwatsa Wata
Rahotonni

Yadda Amurka Ta Yi Kokarin Amfani Da Nukiliya Wajen Tarwatsa Wata

4 days ago
Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya
Rahotonni

Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya

6 days ago
Wata Kungiyar Siyasa Ta Yi Allah Wadai Da Rusau A Jihar Kaduna
Rahotonni

Ragargazar Sallama Da El-Rufa’i Ke Yi A Kaduna

7 days ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari Ya Dawo Nijeriya Daga Landan
Rahotonni

Zaki Da Dacin Mulkin Shugaba Buhari

7 days ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sako Wasu Mutum 2 Da Suka Sace A Wata Cocin Jihar Abiya 

DA DUMI-DUMI: 'Yan Bindiga Sun Sace Wani Basaraken Gargajiya Da Wasu Mutum 3 A Ondo

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

June 3, 2023
Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

June 3, 2023
Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

June 2, 2023
Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

June 2, 2023
Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

June 2, 2023
Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

June 2, 2023
Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

June 2, 2023
Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

June 2, 2023
An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

June 2, 2023
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

June 2, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.