• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa (NLC) ta baiwa gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki bakwai domin ta mayar da duk wasu kuɗaɗen ma’aikata da ake zargin an karkatar daga Asusun NSITF tare da gaggauta kafa hukumar gudanarwa ta Hukumar Fansho ta ƙasa (PENCOM). Ta gargadi cewa kin yin hakan zai jefa kasar cikin rikicin masana’antu.

A wata sanarwa da ta fitar bayan taron kwamitin aiki, wanda shugaban NLC, Kwamared Joe Ajaero ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta zargi gwamnati da tauye haƙƙin ma’aikata da karya dokokin kare kuɗaɗen fansho da taimakon doreszamantakewa. NLC ta nuna fushi kan rahoton karkatar da kaso 40 na kuɗin gudunmawar ma’aikata na NSITF zuwa asusun gwamnati a matsayin kuɗin shiga, tana mai cewa hakan ya sabawa dokar kafa hukumar.

  • Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba
  • ‘Yan Nijeriya Ku Kauracewa Amfani Da Layukan Waya Na MTN, Airtel Da Glo – NLC

Kungiyar ta kuma yi Allah-wadai da yunƙurin gyara dokar NSITF domin baiwa gwamnati cikakken iko kan kuɗaɗen, tana mai gargadin cewa hakan zai tauye ikon ma’aikata kuma ya saɓa ƙa’idojin ƙwadago na ƙasa da ƙasa.

Haka kuma, NLC ta ce rashin kafa hukumar gudanarwa ta PENCOM ya haifar da giɓi a shugabanci, inda kuɗaɗen fansho ke ƙarƙashin ikon jami’an gwamnati kaɗai ba tare da wakilcin ma’aikata da masu ɗaukar ma’aikata ba.

Sanarwar ta ce dole ne a dawo da duk kuɗaɗen da aka karkatar cikin kwanaki bakwai tare da kafa shugabancin hukumar PENCOM bisa ƙa’ida, Idan ba a yi haka ba, NLC ba za ta sake bayar da tabbacin zaman lafiya a masana’antu ba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NlcTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Next Post

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Related

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1
Labarai

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

51 minutes ago
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

2 hours ago
Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin
Manyan Labarai

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

3 hours ago
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

12 hours ago
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano
Labarai

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

12 hours ago
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 
Manyan Labarai

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

13 hours ago
Next Post
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara - Gwamna Lawal Dare

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

September 4, 2025
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

September 4, 2025
Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

September 4, 2025
Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.