• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Yi Mummunar Bari A Arewa Maso Gabas

 Sakatare Da Kakakin Shiyya, Kusoshi Da Dandazo Mambobi Sun Koma PDP

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren jam’iyyar New Nigeria People Party (NNPP) a shiyyar arewa maso gabas, Alhaji Babayo Liman, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar tare da shiga cikin jam’iyyar PDP hade da dumbin magoya bayansa.

 

Ya sanar da cewa, a karkashinsa ya yi rijista wa mambobi sama da miliyan 3.5 a jam’iyyar NNPP a arewa maso gabas cikin shekara takwas, don haka kaso 80 cikin dari na wadannan adadin sun amince da ficewa daga jam’iyyar tare da komawa cikin jam’iyyar PDP.

  • Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan APC Ya Koma PDP A Sakkwato

Liman wanda shi ne Ko’odineta na Kwankwasiyya a jihar Bauchi da Arewa Maso Gabas ya sanar a wani taron manema labarai da ya yi a NUJ da ke Bauchi a ranar Litinin cewa sun yanke wannan shawarar ne domin kishin arewa da ma kasa baki daya.

 

Labarai Masu Nasaba

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

Ya kuma shaida wa ‘yan jaridan cewa daga cikin wadanda suka fice tare da shi daga NNPP sun hada har da shugabar mata ta shiyyar arewa maso gabas, Hajiya Halima Tafawa Balewa; sakataren watsa labarai na jam’iyyar a shiyyar arewwa maso gabas – Ibrahim Abdu; mamba a kwamitin yakin zaben Kwankwaso – Tijjani Hassan da wasu kusoshin jam’iyyar a arewa maso gabas inda suka sanar da komawa PDP.

 

Liman ya ce, a jihar Bauchi kawai mambobi da magoya bayansa sama da dubu 700,000 ne suka mara masa baya wajen fita daga NNPP zuwa PDP domin mara wa Atiku da gwamna Bala Muhammad baya.

 

Liman, ya kara da cewa tun ranar 14 ga watan Janairu ya fice daga jam’iyyar amma ya shelanta wa duniya hakan ne a ranar Litinin bayan yanke matsayar inda ya koma wato PDP, ya nemi sauran magoya bayansu da su biyo shi.

 

Dakta Babayo Liman sannan ya bukaci dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da shi ma kawai ya amince ya koma PDP tare da mara baya wa Atiku Abubakar domin ciyar da kasar nan gaba.

 

Liman wanda tsohon mamba ne a kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na NNPP, ya ce, “Bisa ga wasu dalilai na kokarin ceto kasar nan daga halin da take ciki, in a da ina cikin duhu ni da magoya bayana sama da miliyan 3.5 a arewa maso gabas yanzu Allah ya bude mana ido mun gane gaskiya.

 

“Idan muna son gaskiya, muna son arewa muna son Nijeriya, to ya zama dole mu goya baya wa Wazirin Adamawa, Alhaji Atiku Abubakar. Wannan shi ne babbar dalilin da ya sa na ga ya kamata na jawo mutane ne sama da miliyan uku da suke arewa maso gabas domin mu goya baya wa Atiku ganin cewa lokacin da Obasanjo ya yi mulki Atiku ne mataimakinsa kuma dukkanin nasarorin da aka samu a gwamnatin Obasanjo Atiku ne sila.”

 

A gefe guda kuma ya nemi dukkanin magoya bayansa da su mara baya wa Sanata Bala Muhammad a matakin gwamnan jihar Bauchi. Ya nuna kwarin guiwarsa na cewa tabbas Bala Muhammad idan ya zarce zai ci gaba da shimfida kyawawan ayyukan raya jihar Bauchi.

 

Liman ya kara da cewa muddin jama’a suka zabi Atiku ya tabbata zai yi kokarin magance matsalolin da suke addabar kasar nan da suka hada da matsalar tattalin arziki da tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dabarun Kasar Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Bunkasa Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

Related

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
Siyasa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

3 hours ago
Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC
Siyasa

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

1 day ago
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

2 days ago
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
Labarai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

2 days ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

4 days ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

5 days ago
Next Post
Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.