• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Yi Mummunar Bari A Arewa Maso Gabas

 Sakatare Da Kakakin Shiyya, Kusoshi Da Dandazo Mambobi Sun Koma PDP

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren jam’iyyar New Nigeria People Party (NNPP) a shiyyar arewa maso gabas, Alhaji Babayo Liman, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar tare da shiga cikin jam’iyyar PDP hade da dumbin magoya bayansa.

 

Ya sanar da cewa, a karkashinsa ya yi rijista wa mambobi sama da miliyan 3.5 a jam’iyyar NNPP a arewa maso gabas cikin shekara takwas, don haka kaso 80 cikin dari na wadannan adadin sun amince da ficewa daga jam’iyyar tare da komawa cikin jam’iyyar PDP.

  • Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan APC Ya Koma PDP A Sakkwato

Liman wanda shi ne Ko’odineta na Kwankwasiyya a jihar Bauchi da Arewa Maso Gabas ya sanar a wani taron manema labarai da ya yi a NUJ da ke Bauchi a ranar Litinin cewa sun yanke wannan shawarar ne domin kishin arewa da ma kasa baki daya.

 

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Ya kuma shaida wa ‘yan jaridan cewa daga cikin wadanda suka fice tare da shi daga NNPP sun hada har da shugabar mata ta shiyyar arewa maso gabas, Hajiya Halima Tafawa Balewa; sakataren watsa labarai na jam’iyyar a shiyyar arewwa maso gabas – Ibrahim Abdu; mamba a kwamitin yakin zaben Kwankwaso – Tijjani Hassan da wasu kusoshin jam’iyyar a arewa maso gabas inda suka sanar da komawa PDP.

 

Liman ya ce, a jihar Bauchi kawai mambobi da magoya bayansa sama da dubu 700,000 ne suka mara masa baya wajen fita daga NNPP zuwa PDP domin mara wa Atiku da gwamna Bala Muhammad baya.

 

Liman, ya kara da cewa tun ranar 14 ga watan Janairu ya fice daga jam’iyyar amma ya shelanta wa duniya hakan ne a ranar Litinin bayan yanke matsayar inda ya koma wato PDP, ya nemi sauran magoya bayansu da su biyo shi.

 

Dakta Babayo Liman sannan ya bukaci dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da shi ma kawai ya amince ya koma PDP tare da mara baya wa Atiku Abubakar domin ciyar da kasar nan gaba.

 

Liman wanda tsohon mamba ne a kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na NNPP, ya ce, “Bisa ga wasu dalilai na kokarin ceto kasar nan daga halin da take ciki, in a da ina cikin duhu ni da magoya bayana sama da miliyan 3.5 a arewa maso gabas yanzu Allah ya bude mana ido mun gane gaskiya.

 

“Idan muna son gaskiya, muna son arewa muna son Nijeriya, to ya zama dole mu goya baya wa Wazirin Adamawa, Alhaji Atiku Abubakar. Wannan shi ne babbar dalilin da ya sa na ga ya kamata na jawo mutane ne sama da miliyan uku da suke arewa maso gabas domin mu goya baya wa Atiku ganin cewa lokacin da Obasanjo ya yi mulki Atiku ne mataimakinsa kuma dukkanin nasarorin da aka samu a gwamnatin Obasanjo Atiku ne sila.”

 

A gefe guda kuma ya nemi dukkanin magoya bayansa da su mara baya wa Sanata Bala Muhammad a matakin gwamnan jihar Bauchi. Ya nuna kwarin guiwarsa na cewa tabbas Bala Muhammad idan ya zarce zai ci gaba da shimfida kyawawan ayyukan raya jihar Bauchi.

 

Liman ya kara da cewa muddin jama’a suka zabi Atiku ya tabbata zai yi kokarin magance matsalolin da suke addabar kasar nan da suka hada da matsalar tattalin arziki da tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dabarun Kasar Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Bunkasa Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

18 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

21 hours ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

1 day ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

3 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

4 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

5 days ago
Next Post
Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

LABARAI MASU NASABA

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.