• English
  • Business News
Wednesday, May 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Yi Mummunar Bari A Arewa Maso Gabas

 Sakatare Da Kakakin Shiyya, Kusoshi Da Dandazo Mambobi Sun Koma PDP

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren jam’iyyar New Nigeria People Party (NNPP) a shiyyar arewa maso gabas, Alhaji Babayo Liman, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar tare da shiga cikin jam’iyyar PDP hade da dumbin magoya bayansa.

 

Ya sanar da cewa, a karkashinsa ya yi rijista wa mambobi sama da miliyan 3.5 a jam’iyyar NNPP a arewa maso gabas cikin shekara takwas, don haka kaso 80 cikin dari na wadannan adadin sun amince da ficewa daga jam’iyyar tare da komawa cikin jam’iyyar PDP.

  • Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan APC Ya Koma PDP A Sakkwato

Liman wanda shi ne Ko’odineta na Kwankwasiyya a jihar Bauchi da Arewa Maso Gabas ya sanar a wani taron manema labarai da ya yi a NUJ da ke Bauchi a ranar Litinin cewa sun yanke wannan shawarar ne domin kishin arewa da ma kasa baki daya.

 

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

Ya kuma shaida wa ‘yan jaridan cewa daga cikin wadanda suka fice tare da shi daga NNPP sun hada har da shugabar mata ta shiyyar arewa maso gabas, Hajiya Halima Tafawa Balewa; sakataren watsa labarai na jam’iyyar a shiyyar arewwa maso gabas – Ibrahim Abdu; mamba a kwamitin yakin zaben Kwankwaso – Tijjani Hassan da wasu kusoshin jam’iyyar a arewa maso gabas inda suka sanar da komawa PDP.

 

Liman ya ce, a jihar Bauchi kawai mambobi da magoya bayansa sama da dubu 700,000 ne suka mara masa baya wajen fita daga NNPP zuwa PDP domin mara wa Atiku da gwamna Bala Muhammad baya.

 

Liman, ya kara da cewa tun ranar 14 ga watan Janairu ya fice daga jam’iyyar amma ya shelanta wa duniya hakan ne a ranar Litinin bayan yanke matsayar inda ya koma wato PDP, ya nemi sauran magoya bayansu da su biyo shi.

 

Dakta Babayo Liman sannan ya bukaci dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da shi ma kawai ya amince ya koma PDP tare da mara baya wa Atiku Abubakar domin ciyar da kasar nan gaba.

 

Liman wanda tsohon mamba ne a kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na NNPP, ya ce, “Bisa ga wasu dalilai na kokarin ceto kasar nan daga halin da take ciki, in a da ina cikin duhu ni da magoya bayana sama da miliyan 3.5 a arewa maso gabas yanzu Allah ya bude mana ido mun gane gaskiya.

 

“Idan muna son gaskiya, muna son arewa muna son Nijeriya, to ya zama dole mu goya baya wa Wazirin Adamawa, Alhaji Atiku Abubakar. Wannan shi ne babbar dalilin da ya sa na ga ya kamata na jawo mutane ne sama da miliyan uku da suke arewa maso gabas domin mu goya baya wa Atiku ganin cewa lokacin da Obasanjo ya yi mulki Atiku ne mataimakinsa kuma dukkanin nasarorin da aka samu a gwamnatin Obasanjo Atiku ne sila.”

 

A gefe guda kuma ya nemi dukkanin magoya bayansa da su mara baya wa Sanata Bala Muhammad a matakin gwamnan jihar Bauchi. Ya nuna kwarin guiwarsa na cewa tabbas Bala Muhammad idan ya zarce zai ci gaba da shimfida kyawawan ayyukan raya jihar Bauchi.

 

Liman ya kara da cewa muddin jama’a suka zabi Atiku ya tabbata zai yi kokarin magance matsalolin da suke addabar kasar nan da suka hada da matsalar tattalin arziki da tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dabarun Kasar Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Bunkasa Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

Related

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 days ago
Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
Ilimi

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

3 days ago
Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya
Siyasa

Majalisar Wakilai Ta Yi Watsi Da Kafa Dokar Karba-karba A Shugabancin Nijeriya

4 days ago
A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC
Siyasa

A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC

5 days ago
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

6 days ago
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

1 week ago
Next Post
Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

LABARAI MASU NASABA

Za A Gudanar Da Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Karo Na 4 A Birnin Changsha Dake Lardin Hunan

Za A Gudanar Da Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Karo Na 4 A Birnin Changsha Dake Lardin Hunan

May 21, 2025
zulum

‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Sojoji Da ‘Yan Siyasa Wajen Samun Bayanan Sirri – Zulum 

May 21, 2025
Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

May 21, 2025
Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara

Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara

May 21, 2025
Hajjin Bana: Jihar Filato Ta Ba Da Kyautar Kujera 500 Da Tallafin Miliyan 2 Ga Duk Maniyyaci

Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya 

May 21, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Matasa 2 Da Ake Zargi Da Satar Mota A Kebbi

May 21, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN

Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN

May 21, 2025
Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar

Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar

May 21, 2025
An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka

An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka

May 21, 2025
Sarkin Yawa Ya Fi Sarkin Karfi

Sarkin Yawa Ya Fi Sarkin Karfi

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.