ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Yi Mummunar Bari A Arewa Maso Gabas

 Sakatare Da Kakakin Shiyya, Kusoshi Da Dandazo Mambobi Sun Koma PDP

by Khalid Idris Doya
3 years ago

Sakataren jam’iyyar New Nigeria People Party (NNPP) a shiyyar arewa maso gabas, Alhaji Babayo Liman, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar tare da shiga cikin jam’iyyar PDP hade da dumbin magoya bayansa.

 

Ya sanar da cewa, a karkashinsa ya yi rijista wa mambobi sama da miliyan 3.5 a jam’iyyar NNPP a arewa maso gabas cikin shekara takwas, don haka kaso 80 cikin dari na wadannan adadin sun amince da ficewa daga jam’iyyar tare da komawa cikin jam’iyyar PDP.

ADVERTISEMENT
  • Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan APC Ya Koma PDP A Sakkwato

Liman wanda shi ne Ko’odineta na Kwankwasiyya a jihar Bauchi da Arewa Maso Gabas ya sanar a wani taron manema labarai da ya yi a NUJ da ke Bauchi a ranar Litinin cewa sun yanke wannan shawarar ne domin kishin arewa da ma kasa baki daya.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Ya kuma shaida wa ‘yan jaridan cewa daga cikin wadanda suka fice tare da shi daga NNPP sun hada har da shugabar mata ta shiyyar arewa maso gabas, Hajiya Halima Tafawa Balewa; sakataren watsa labarai na jam’iyyar a shiyyar arewwa maso gabas – Ibrahim Abdu; mamba a kwamitin yakin zaben Kwankwaso – Tijjani Hassan da wasu kusoshin jam’iyyar a arewa maso gabas inda suka sanar da komawa PDP.

 

Liman ya ce, a jihar Bauchi kawai mambobi da magoya bayansa sama da dubu 700,000 ne suka mara masa baya wajen fita daga NNPP zuwa PDP domin mara wa Atiku da gwamna Bala Muhammad baya.

 

Liman, ya kara da cewa tun ranar 14 ga watan Janairu ya fice daga jam’iyyar amma ya shelanta wa duniya hakan ne a ranar Litinin bayan yanke matsayar inda ya koma wato PDP, ya nemi sauran magoya bayansu da su biyo shi.

 

Dakta Babayo Liman sannan ya bukaci dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da shi ma kawai ya amince ya koma PDP tare da mara baya wa Atiku Abubakar domin ciyar da kasar nan gaba.

 

Liman wanda tsohon mamba ne a kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na NNPP, ya ce, “Bisa ga wasu dalilai na kokarin ceto kasar nan daga halin da take ciki, in a da ina cikin duhu ni da magoya bayana sama da miliyan 3.5 a arewa maso gabas yanzu Allah ya bude mana ido mun gane gaskiya.

 

“Idan muna son gaskiya, muna son arewa muna son Nijeriya, to ya zama dole mu goya baya wa Wazirin Adamawa, Alhaji Atiku Abubakar. Wannan shi ne babbar dalilin da ya sa na ga ya kamata na jawo mutane ne sama da miliyan uku da suke arewa maso gabas domin mu goya baya wa Atiku ganin cewa lokacin da Obasanjo ya yi mulki Atiku ne mataimakinsa kuma dukkanin nasarorin da aka samu a gwamnatin Obasanjo Atiku ne sila.”

 

A gefe guda kuma ya nemi dukkanin magoya bayansa da su mara baya wa Sanata Bala Muhammad a matakin gwamnan jihar Bauchi. Ya nuna kwarin guiwarsa na cewa tabbas Bala Muhammad idan ya zarce zai ci gaba da shimfida kyawawan ayyukan raya jihar Bauchi.

 

Liman ya kara da cewa muddin jama’a suka zabi Atiku ya tabbata zai yi kokarin magance matsalolin da suke addabar kasar nan da suka hada da matsalar tattalin arziki da tsaro.

Arewa maso gabas
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

Yadda Ake Gyaran Gashi Na Musamman

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.