• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noma: Gwamnan Zamfara Ya Nemo Masu Zuba Jari Daga Ƙasar Turkiyya

by Leadership Hausa
12 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Noma: Gwamnan Zamfara Ya Nemo Masu Zuba Jari Daga Ƙasar Turkiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya samu nasarar jawo hankalin wasu jiga-jigan masu zuba jari ‘yan ƙasar Turkiyya don su zuba jarin su a Zamfara.

A ziyarar da ya kai ƙasar ta Turkiyya a farkon watannan na Yuli, Gwamna Lawal ya samu ganawa da wasu masu zuba jari a ƙasar, tare da kai ziyarorin gani da ido a garuruwa daban-daban.

  • Sheikh Daurawa Ya Yi Kira Ga Musulmi Da Su Nisanci Zanga-zanga Kan Adawa Da Tsadar Rayuwa

 

Kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu yau a Gusau cewa, Gwamna Lawal ya fara wannan ziyarar aiki a ƙasar Turkiyya ne a ranar Lahadi, 30 ga watan Yunin nan da ya gabata, inda ya kwashe kwana shida a can.

zamfara

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

Sanarwar ta Malam Idris ta kuma bayyana cewa, gwamnan da muƙarrabansa, sun ziyarci wurare da dama, waɗanda suka haɗa da wuraren kayan amfanin gona na zamani, wurin samar da nonon shanu, kiwon kaji da kamfanin ƙera motocin noma (Tarakta) na ‘Turk Traktor (tractors) manufacturing plant.’

“A wannan ziyarar aiki ta Turkiyya, Gwamna Lawal ya fara ne da kai ziyara a Bursa City, inda kamfanin Direkci Group ke da wurin Kayan amfanin gona na zamani mafi girma a ƙasar, inda shugaban kamfanin na Direkci Group, Mehmet Nurullah Direkçi, da kan shi ya zagaya da gwamnan cikin wannan katafaren wuri.

zamfara

“Shi wannan kamfani na Direkci Group, yana samar da harkokin noma ga ƙasar ta Turkiyya da sauran masu zuba jari ta hanyar kanyan amfanin gona na zamani. Kamfanin zai samar da irin wannan shirin kayan amfanin gona na zamani a jihar Zamfara.

“Idan wannan kamfani na Direkci Group ya shigo Zamfara, zai samar da kayan amfanin gona na zamani kala-kala, waɗanda suka haɗa da noman zamani mara iri, noman zamani mai iri, dashen shuka, noman ayaba na zamani dai sauran harkokin noma na zamani”.

zamfara

Yayin da yake a birnin Gaziantep, Gwamna Lawal ya ziyarci gonar noman madara ta Innova Dairy, wacce ke ba da shawarwari da sabbin hanyoyin kafawa da sarrafa gonakin zamani yadda ya kamata.

“Gonar ta Innova Dairy Farm za ta kafa wani tsari a Jihar Zamfara don amfani da duk fasahohin zamani da suka haɗa da Kiwon Shanu na Zamani, Tsarin Kula da Garken Dabbabi, Tatsar Madarar Shanu, Sarrafa Taki da kayan aikin gona.”

zamfara

A Lardin Sakarya, Gwamna Lawal da tawagarsa sun ziyarci masana’antar sarrafa taraktoci ta TurkTraktor domin tantance tsarin samar da taraktocin da suka dace da noma a Nijeriya.

“A masana’antar Turk Traktor, Gwamna Lawal ya tattauna yiwuwar haɗin gwiwa da kamfanin domin ba iwa Jihar Zamfara damar samun waɗannan taraktoci na zamani.

“Turk Traktor yana da ikon samar da taraktoci ta zamani. Kamfanin dai shi ne kamfani na farko da ke fitar da taraktoci a ƙasar Turkiyya kuma ya kai kashi 88 bisa 100 na adadin taraktocin da ƙasar ke fitarwa a shekarar 2022.

zamfara

“TurkTraktor babban kamfani ne na duniya, wanda ke fitar da taraktoci zuwa ƙasashe 125, kuma yana samar da kusan kashi 80 bisa 100 na adadin kayayyaki zuwa kasuwannin Arewacin Amurka da Turai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BunkasaCi GabaNijeriyaNomaTurkiyyaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Tura Tsohon Ministan Wutar Lantarki Zuwa Gidan Yari

Next Post

Tinubu, Shettima Da Gwamnonin Na Ganawar Sirri

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

4 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

4 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

5 days ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

6 days ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 weeks ago
Next Post
Tinubu, Shettima Da Gwamnonin Na Ganawar Sirri

Tinubu, Shettima Da Gwamnonin Na Ganawar Sirri

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.