• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noma: Gwamnan Zamfara Ya Nemo Masu Zuba Jari Daga Ƙasar Turkiyya

by Leadership Hausa
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Noma: Gwamnan Zamfara Ya Nemo Masu Zuba Jari Daga Ƙasar Turkiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya samu nasarar jawo hankalin wasu jiga-jigan masu zuba jari ‘yan ƙasar Turkiyya don su zuba jarin su a Zamfara.

A ziyarar da ya kai ƙasar ta Turkiyya a farkon watannan na Yuli, Gwamna Lawal ya samu ganawa da wasu masu zuba jari a ƙasar, tare da kai ziyarorin gani da ido a garuruwa daban-daban.

  • Sheikh Daurawa Ya Yi Kira Ga Musulmi Da Su Nisanci Zanga-zanga Kan Adawa Da Tsadar Rayuwa

 

Kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu yau a Gusau cewa, Gwamna Lawal ya fara wannan ziyarar aiki a ƙasar Turkiyya ne a ranar Lahadi, 30 ga watan Yunin nan da ya gabata, inda ya kwashe kwana shida a can.

zamfara

Labarai Masu Nasaba

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

Sanarwar ta Malam Idris ta kuma bayyana cewa, gwamnan da muƙarrabansa, sun ziyarci wurare da dama, waɗanda suka haɗa da wuraren kayan amfanin gona na zamani, wurin samar da nonon shanu, kiwon kaji da kamfanin ƙera motocin noma (Tarakta) na ‘Turk Traktor (tractors) manufacturing plant.’

“A wannan ziyarar aiki ta Turkiyya, Gwamna Lawal ya fara ne da kai ziyara a Bursa City, inda kamfanin Direkci Group ke da wurin Kayan amfanin gona na zamani mafi girma a ƙasar, inda shugaban kamfanin na Direkci Group, Mehmet Nurullah Direkçi, da kan shi ya zagaya da gwamnan cikin wannan katafaren wuri.

zamfara

“Shi wannan kamfani na Direkci Group, yana samar da harkokin noma ga ƙasar ta Turkiyya da sauran masu zuba jari ta hanyar kanyan amfanin gona na zamani. Kamfanin zai samar da irin wannan shirin kayan amfanin gona na zamani a jihar Zamfara.

“Idan wannan kamfani na Direkci Group ya shigo Zamfara, zai samar da kayan amfanin gona na zamani kala-kala, waɗanda suka haɗa da noman zamani mara iri, noman zamani mai iri, dashen shuka, noman ayaba na zamani dai sauran harkokin noma na zamani”.

zamfara

Yayin da yake a birnin Gaziantep, Gwamna Lawal ya ziyarci gonar noman madara ta Innova Dairy, wacce ke ba da shawarwari da sabbin hanyoyin kafawa da sarrafa gonakin zamani yadda ya kamata.

“Gonar ta Innova Dairy Farm za ta kafa wani tsari a Jihar Zamfara don amfani da duk fasahohin zamani da suka haɗa da Kiwon Shanu na Zamani, Tsarin Kula da Garken Dabbabi, Tatsar Madarar Shanu, Sarrafa Taki da kayan aikin gona.”

zamfara

A Lardin Sakarya, Gwamna Lawal da tawagarsa sun ziyarci masana’antar sarrafa taraktoci ta TurkTraktor domin tantance tsarin samar da taraktocin da suka dace da noma a Nijeriya.

“A masana’antar Turk Traktor, Gwamna Lawal ya tattauna yiwuwar haɗin gwiwa da kamfanin domin ba iwa Jihar Zamfara damar samun waɗannan taraktoci na zamani.

“Turk Traktor yana da ikon samar da taraktoci ta zamani. Kamfanin dai shi ne kamfani na farko da ke fitar da taraktoci a ƙasar Turkiyya kuma ya kai kashi 88 bisa 100 na adadin taraktocin da ƙasar ke fitarwa a shekarar 2022.

zamfara

“TurkTraktor babban kamfani ne na duniya, wanda ke fitar da taraktoci zuwa ƙasashe 125, kuma yana samar da kusan kashi 80 bisa 100 na adadin kayayyaki zuwa kasuwannin Arewacin Amurka da Turai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BunkasaCi GabaNijeriyaNomaTurkiyyaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Tura Tsohon Ministan Wutar Lantarki Zuwa Gidan Yari

Next Post

Tinubu, Shettima Da Gwamnonin Na Ganawar Sirri

Related

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

6 days ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

6 days ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

2 weeks ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

3 weeks ago
Next Post
Tinubu, Shettima Da Gwamnonin Na Ganawar Sirri

Tinubu, Shettima Da Gwamnonin Na Ganawar Sirri

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.