• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PRP Ta Yi Gargadi Kan Kafa Sansanonin Sojojin Kasashen Waje A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
PRP Ta Yi Gargadi Kan Kafa Sansanonin Sojojin Kasashen Waje A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PRP ta bi sahun ‘yan Nijeriya wajen gargadin gwamnatin tarayya kan gayyato sojojin Amurka da wasu sauran kasashen Turai domin su kafa sansanoninsu na soja a Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar tare da sa hannun mukaddashin sakataren yada labaranta na kasa, Kwamared Muhammed Ishak, ta ce barin sojojin kasashen waje su shigo Nijeriya bayan an kore su daga wasu kasashe kamar irinsu Senegal da Nigarr babban hatsari ne ga tsaron kasa da kuma lafiyar ‘yan Nijeriya.

  • CBN Ya Bayyana Sunayen Bankuna 41 Da Ya Aminta Da Ingancinsu A Nijeriya 
  • Sinawa Ba Za Su Manta Da Danyen Laifin NATO Na Kai Wa Yugoslavia Hari Ba

Jam’iyyar ta bukaci gwamnatin tarayya ta yi watsi da irin wannnan tunani domin bai dace da manufar kasa ba, saboda baraza ce ga ‘yancin Nijeriya da tattalin arziki da difilomasiyya na tusa manufar kasashen waje cikin kasa mai ‘yancin gashin kai kamar Nijeriya.

“Jam’iyyar PRP ta bi sahun ‘yan Nijeriya wajen jawo hankalin Shugaban kasa, Bola Tinubu da majalisar kasa kan illar gayyato sojojin Amurka da wasu kasashen Turai na kafa sassanin soja a Nijeriya, bayan da aka fatattake su daga wasu kasashe.

“Matsayar jam’iyyar PRP kan wannan yunkurin dai shi ne, akwai matukar illa ga sha’anin tsaron kasarmu da ‘yancin gashin kai. Domin haka ne muke gargadin gwamnatin Nijeriya ba ma goyon bayan wannan lamari.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

“Gayyato wadannan sojoji zuwa kasarmu domin su kafa sassani ba karamin illa ba ce ga harkokin tsaronmu da kuma lafiyar ‘yan ksarmu. Bisa tsarin da aka kafa jam’iyyarmu na samun cikakken ‘yanci, wannan ya saba da ra’ayin kasarmu saboda dalilai da dama.

“Shigowar sojojin zai kara tauye ‘yancinmu wajen shigo da ra’ayoyin ‘yan kasashen ketare a kasarmu ta gado. Sannan za a samu sabon barazana kan harkokin tsaro, domin wadannan sojojin ba su san sha’anin tsaron Nijeriya ba wanda haka ka iya janyo hatsarin ta’addanci da sauran rikice-rikice.

“Dole ne gwamnatin Nijeriya ta yi la’akari da illar da wannan lamari zai yi wa tattalin arziki idan hharr sojojin kasashen waje suka kafa sassaninsu a Nijeriya. Za a samu tsadar masaukin sojojin da kulawa da ababen more rayuwarsu. Bugu da kari, akwai babban illa wajenn kulawa da sojojin kasashen ketare.”

Sai dai kuma, Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris Malagi, ya musanta cewa Nijeriya na shirin amincewa a kafa sansanonin sojin na kasashen waje a kasarta, yana mai cewar masu yamadidi ne kawai suka kitsa maganar kuma suke ta yadawa.

“Ina mai tabbatar wa da ‘yan kasa cewa babu wannan shirin. Akwai kasashen da muke kawance da su don yaki da matsalar tsaronmu, wannan muna ci gaba da yi, amma ba wai batun kafa sansanonin sojojinsu. Jita-jita ce kawai!”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GargadiPDPSansanin Sojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Ban Kwana Da Firaministan Hungary Ya Shirya Masa

Next Post

Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

LABARAI MASU NASABA

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.