• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PRP Ta Yi Gargadi Kan Kafa Sansanonin Sojojin Kasashen Waje A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
PRP Ta Yi Gargadi Kan Kafa Sansanonin Sojojin Kasashen Waje A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PRP ta bi sahun ‘yan Nijeriya wajen gargadin gwamnatin tarayya kan gayyato sojojin Amurka da wasu sauran kasashen Turai domin su kafa sansanoninsu na soja a Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar tare da sa hannun mukaddashin sakataren yada labaranta na kasa, Kwamared Muhammed Ishak, ta ce barin sojojin kasashen waje su shigo Nijeriya bayan an kore su daga wasu kasashe kamar irinsu Senegal da Nigarr babban hatsari ne ga tsaron kasa da kuma lafiyar ‘yan Nijeriya.

  • CBN Ya Bayyana Sunayen Bankuna 41 Da Ya Aminta Da Ingancinsu A Nijeriya 
  • Sinawa Ba Za Su Manta Da Danyen Laifin NATO Na Kai Wa Yugoslavia Hari Ba

Jam’iyyar ta bukaci gwamnatin tarayya ta yi watsi da irin wannnan tunani domin bai dace da manufar kasa ba, saboda baraza ce ga ‘yancin Nijeriya da tattalin arziki da difilomasiyya na tusa manufar kasashen waje cikin kasa mai ‘yancin gashin kai kamar Nijeriya.

“Jam’iyyar PRP ta bi sahun ‘yan Nijeriya wajen jawo hankalin Shugaban kasa, Bola Tinubu da majalisar kasa kan illar gayyato sojojin Amurka da wasu kasashen Turai na kafa sassanin soja a Nijeriya, bayan da aka fatattake su daga wasu kasashe.

“Matsayar jam’iyyar PRP kan wannan yunkurin dai shi ne, akwai matukar illa ga sha’anin tsaron kasarmu da ‘yancin gashin kai. Domin haka ne muke gargadin gwamnatin Nijeriya ba ma goyon bayan wannan lamari.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

“Gayyato wadannan sojoji zuwa kasarmu domin su kafa sassani ba karamin illa ba ce ga harkokin tsaronmu da kuma lafiyar ‘yan ksarmu. Bisa tsarin da aka kafa jam’iyyarmu na samun cikakken ‘yanci, wannan ya saba da ra’ayin kasarmu saboda dalilai da dama.

“Shigowar sojojin zai kara tauye ‘yancinmu wajen shigo da ra’ayoyin ‘yan kasashen ketare a kasarmu ta gado. Sannan za a samu sabon barazana kan harkokin tsaro, domin wadannan sojojin ba su san sha’anin tsaron Nijeriya ba wanda haka ka iya janyo hatsarin ta’addanci da sauran rikice-rikice.

“Dole ne gwamnatin Nijeriya ta yi la’akari da illar da wannan lamari zai yi wa tattalin arziki idan hharr sojojin kasashen waje suka kafa sassaninsu a Nijeriya. Za a samu tsadar masaukin sojojin da kulawa da ababen more rayuwarsu. Bugu da kari, akwai babban illa wajenn kulawa da sojojin kasashen ketare.”

Sai dai kuma, Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris Malagi, ya musanta cewa Nijeriya na shirin amincewa a kafa sansanonin sojin na kasashen waje a kasarta, yana mai cewar masu yamadidi ne kawai suka kitsa maganar kuma suke ta yadawa.

“Ina mai tabbatar wa da ‘yan kasa cewa babu wannan shirin. Akwai kasashen da muke kawance da su don yaki da matsalar tsaronmu, wannan muna ci gaba da yi, amma ba wai batun kafa sansanonin sojojinsu. Jita-jita ce kawai!”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GargadiPDPSansanin Sojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Ban Kwana Da Firaministan Hungary Ya Shirya Masa

Next Post

Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

6 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.