• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PRP Ta Yi Gargadi Kan Kafa Sansanonin Sojojin Kasashen Waje A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
PRP Ta Yi Gargadi Kan Kafa Sansanonin Sojojin Kasashen Waje A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PRP ta bi sahun ‘yan Nijeriya wajen gargadin gwamnatin tarayya kan gayyato sojojin Amurka da wasu sauran kasashen Turai domin su kafa sansanoninsu na soja a Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar tare da sa hannun mukaddashin sakataren yada labaranta na kasa, Kwamared Muhammed Ishak, ta ce barin sojojin kasashen waje su shigo Nijeriya bayan an kore su daga wasu kasashe kamar irinsu Senegal da Nigarr babban hatsari ne ga tsaron kasa da kuma lafiyar ‘yan Nijeriya.

  • CBN Ya Bayyana Sunayen Bankuna 41 Da Ya Aminta Da Ingancinsu A Nijeriya 
  • Sinawa Ba Za Su Manta Da Danyen Laifin NATO Na Kai Wa Yugoslavia Hari Ba

Jam’iyyar ta bukaci gwamnatin tarayya ta yi watsi da irin wannnan tunani domin bai dace da manufar kasa ba, saboda baraza ce ga ‘yancin Nijeriya da tattalin arziki da difilomasiyya na tusa manufar kasashen waje cikin kasa mai ‘yancin gashin kai kamar Nijeriya.

“Jam’iyyar PRP ta bi sahun ‘yan Nijeriya wajen jawo hankalin Shugaban kasa, Bola Tinubu da majalisar kasa kan illar gayyato sojojin Amurka da wasu kasashen Turai na kafa sassanin soja a Nijeriya, bayan da aka fatattake su daga wasu kasashe.

“Matsayar jam’iyyar PRP kan wannan yunkurin dai shi ne, akwai matukar illa ga sha’anin tsaron kasarmu da ‘yancin gashin kai. Domin haka ne muke gargadin gwamnatin Nijeriya ba ma goyon bayan wannan lamari.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

“Gayyato wadannan sojoji zuwa kasarmu domin su kafa sassani ba karamin illa ba ce ga harkokin tsaronmu da kuma lafiyar ‘yan ksarmu. Bisa tsarin da aka kafa jam’iyyarmu na samun cikakken ‘yanci, wannan ya saba da ra’ayin kasarmu saboda dalilai da dama.

“Shigowar sojojin zai kara tauye ‘yancinmu wajen shigo da ra’ayoyin ‘yan kasashen ketare a kasarmu ta gado. Sannan za a samu sabon barazana kan harkokin tsaro, domin wadannan sojojin ba su san sha’anin tsaron Nijeriya ba wanda haka ka iya janyo hatsarin ta’addanci da sauran rikice-rikice.

“Dole ne gwamnatin Nijeriya ta yi la’akari da illar da wannan lamari zai yi wa tattalin arziki idan hharr sojojin kasashen waje suka kafa sassaninsu a Nijeriya. Za a samu tsadar masaukin sojojin da kulawa da ababen more rayuwarsu. Bugu da kari, akwai babban illa wajenn kulawa da sojojin kasashen ketare.”

Sai dai kuma, Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris Malagi, ya musanta cewa Nijeriya na shirin amincewa a kafa sansanonin sojin na kasashen waje a kasarta, yana mai cewar masu yamadidi ne kawai suka kitsa maganar kuma suke ta yadawa.

“Ina mai tabbatar wa da ‘yan kasa cewa babu wannan shirin. Akwai kasashen da muke kawance da su don yaki da matsalar tsaronmu, wannan muna ci gaba da yi, amma ba wai batun kafa sansanonin sojojinsu. Jita-jita ce kawai!”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GargadiPDPSansanin Sojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Ban Kwana Da Firaministan Hungary Ya Shirya Masa

Next Post

Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

2 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
PRP
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

LABARAI MASU NASABA

Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.