ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayi: Ba Na Shakkar Gwabzawa Da Kowa A Takarar Gwamnan Gombe – Mailantarki

by Sulaiman
4 years ago
Mailantarki

Ayau shafinmu na ra’ayi ya tattauna ne da Aliyu Suleiman inda ya ce, mai gidan shi Khamisu Mailantarki dan takarar gwamna a jam’iyyar NNPP baya shakkun fitowa takara da Gwamna mai mulki, ko kuma gwamnatin da ke kan mulki.

 

Wannan kuwa ba abin mamaki ba ne, domin a baya Mailantarki ya nuna cewa shi mutum ne mai jama’a. Su kuma jama’a su ne kasuwa, ba yawan rumfuna ba.

ADVERTISEMENT

 

“A baya abu ne mai wahala a fito yin kokawar gaba-da-gaba da gwamna mai mulki a Jihar Gombe. Amma yanzu abu ne mai sauƙi, kuma idan mu ka yi gaba-da-gaba, mu ka haɗa ƙwanji a ranar zaɓe, to kayar da gwamna abu ne mai sauƙi a wuri na.” Inji Mailantarki, bayan an tsayar da shi takarar gwamna a ƙarƙashin NNPP.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

 

Daga cikin laƙanin da Mailantarki ke taƙama da su, akwai jama’a, waɗanda su ne ya ce su ka roƙe shi ya fito takarar gwamna, domin su sake yi masa irin ruwa da ƙanƙarar yawan ƙuri’un da su ka taɓa yi masa a 2011. Wannan karon ma gaba ɗayan jihar ce, ba wai a ƙananan hukumomi 3 kamar na zaɓen 2011 ba.

 

Wani laƙanin da Mailantarki ya ce ya ke taƙama da shi, shi ne iƙirarin sa cewa gwamnatin APC ba ta tsinana wa Gwambawa abin a zo a gani har a yaba ba.

 

Ba wai girma ake buƙata ga wuƙar da za a feɗe giwa ba, a’a, mai kaifi ake nema komai ƙanƙantar ta.

 

Yayin da ake gwabza yaƙin neman zaɓen gwamnoni a faɗin jihohin Najeriya, zaɓen da zai kasance cikin sahun gaba wanda za a yi kallon kwatagwangwamar kokawa a Arewa, shi ne zaɓen gwamnan Jihar Gombe, wanda a cikin ‘yan takara har da Khamisu Mailantarki, wanda jam’iyyar NNPP ta tsayar takarar gwamna a Gombe.

 

Kada mai karatu ya yi shakku, tababa ko tantama cewa Mailantarki zai iya kayar da Gwamna Inuwa Yahaya a zaɓen 2023. Wanda bai san Mailantarki ba, shi ne zai tsaya ya na wasiwasin wannan nazari.

 

A zaɓen 2011, Mailantarki ya fito takarar Ɗan Majalisar Wakilai ta Ƙasa a Majalisar Tarayya a ƙarƙashin CPC, jam’iyya maras galihu a lokacin. Me ya faru, talakawa da masu halin Ƙananan Hukumomin Gombe/Kwami/Funakaye sun zuba masa ƙuri’un da babu wani Ɗan Majalisa da ya samu kusan yawan ta shi a 2011, kakaf ɗin su har su 360 a Najeriya.

 

Yayin da Mailantarki ya samu ƙuri’u *122,987*, abokin takarar sa na PDP kuwa ƙuri’a 44,206 ya samu. Shi kuma na ANPP ya tashi da ƙuri’un da ba su wuce a jefa cikin aljihun riga malum-malum ba, wato guda 8,760 kacal.

 

Fitar Mailantarki daga APC a cikin watan Mayu, 2022 ke da wuya, sai NNPP ta ba shi takarar gwamna.

 

Alamomin Mailantarki zai firgita manyan namun dajin siyasar Gombe na cikin gwamnati ta fara ne tun daga lokacin da NNPP ta ba shi takara babu hamayya. Wakilai 342 daga Ƙananan Hukumomi 11 duk su ka amince da shi, babu hamayya.

 

Sannan kuma shi da kan sa bayan ya lashe zaɓen fidda-gwanin da wakilai 342 ɗin zu ka zaɓe shi, ya ce, “a tarihin Jihar Gombe ba a taɓa yin zaɓen fidda-gwanin da ya kai na sa zama sahihi ba. Wannan ma alama ce mai nuni da cewa Mailantarki ya samu tagomashi a faɗin jihar kenan.

 

Ko ma dai me ke nan, ganin yadda guguwar Mailantarki ke kwashe manya da ƙananan ‘yan APC da PDP, su na watsi da laima da tsintsiya su na rungumar kwandon kayan marmari, hakan alama ce mai nuna cewa za a kwashi ‘yan kallo a ranar kokawar zaɓen 2023.

 

Tabbas Gwamna Inuwa Yahaya na da aiki a gaban sa. Kuma duk irin inuwar da Inuwa ya shiga da rana, to zai kasance cikin tunanin hasken Mailantarki. Duk cikin duhun da Inuwa Yahaya ya shiga da dare, sai ya yi tunanin hasken Mailantarki. Kai, ko cikin hasken lantarki ko hasken taurari da farin wata Inuwa Yahaya na APC ya shiga, zai ya riƙa tuna hasken Mailantarki.

 

Farin jinin Mailantarki zai iya sakar wa sauran ‘yan takara sukuntumau, ta yadda ko haske fitilar cocila su ka gani, su ce hasken lantarkin Mailantarki ne

 

Wataƙila ma ko a mafarki, ba zai rasa yin mafarkin hasken lantarkin Mailantarki ba.

Mailantarki
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Umarnin Kotu: Gwamnatin Kano Ta Kulle Masallatai Da Makarantar Abduljabbar Kabara

Umarnin Kotu: Gwamnatin Kano Ta Kulle Masallatai Da Makarantar Abduljabbar Kabara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.