• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

by Abubakar Abba and Sulaiman
7 months ago
in Ra'ayoyi
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata 1 ga watan Oktoba Nijeriya ta yi bikin cika shekara 64 da samun mulkin kai daga Turawa. Wasu ‘yan Nijeriya sun bayyana yadda suke ji da kuma fatan da suke da shi a kan wannan biki. Yayin da wasu ke cewa Nijeriya ta cikia burin a daidai wannan lokaci wasu kuma na ganin samsam Nijeriya bata yi abin azo a gani ba musamman in aka lura da wasu kasashe tsasrarrakin kasar nan, wadanda muka samu ‘yancin kai a kusan lokaci daya amma sun yi mana wajen ci gaba da bunkasar tattalin arziki ga dai yadda suka bayyana ra’ayoyin na su.

 

Alh. Adamu Muhammed Makarfi: Mai fashin baki a al’amuran yau da kullum. A nawa ra’ayin, koda ma gwamnatin ta bayyana cewa, ba za ta gudanar da shagulgulan bikin zagayowar ranar ta samun ‘yancin kan Nijeriya ba, koma za ta yi dai, akasarin ‘yan kasar musamman talakawa da bas u iya ciyar da iyalansu sau uku a rana, babu wani da zai damu da wani maganar zagoyowar ranar.

  • Wakilin Sin Ya Bukaci Sassan Somaliya Da Su Kara Azamar Warware Sabani Ta Hanyar Tattaunawa
  • Habasha Ta Jinjinawa Masu Zuba Jari Na Kasar Sin

Tun daga badi zuwa yau, da gwamnatin ta hau karagar mulkin kasar, babu wani abu da sauya na ci gaba, illama ma dai, sai kara jefa akasarin ‘yan kasar da gwamnatin ta yi a cikin ukubar rayuwa, musamman ta hanyar cire tallafin man fetur da ta yi.

 

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Irin wadannan tsauraran tsare-tsaren da gwamnatin ta zo da su, sun kara tagyyar rayuwar talakawan kasar.

 

Hajiya Aisha Abubakar :Shugabar gidauniyar Zulifata da ke a jihar Kaduna da ke sasanta ma’aurata da kwatowa kananan yara hakkinsu, ta ce, a kullum kwannan duniya a gidauniyra mu, muna karbar korafe korafe iri-iri daga gun mata kan yadda mazajensu ke gaza ciyar da iyalansu, duk wannan zan iya cewa, ya samu asali ne daga irin tsararan tsare-tsaren da gwamnatin ta zo da su, musamman kara farashin man feutr da kuma cire tallafin mai.

 

Ta ce, karain abun takaici shi ne, yadda wasu magindantan ke bin dare, suna shiga cikin gonakai domin satar kayan amfanin gona da manoma suka girbe domin su ciyar da iyalansu.

 

Yau ko da magidanci dan kasuwa ne, ko da yaje kasuwar, babu wani gwabbaban ciniki da zai yi da zai iya kula da rayuwar iyalansa.

 

Malam Zakari Adamu: Shi kuwa wani malami a kwaleji kimiyya da fasaha ta tarayya da ke a Jihar Kaduna Malam Zakari Adamu ya ce, a nasa ra’ayin har yanzu gwamnatin da lamau ba ta dauki hanyar samarwa da ‘yan kasar sauki ba domin kuwa, a kullum tunaninta, kara karkata yake a kan jefa ‘yan kasar a cikin kunci ta hanyar fito da tsare-tsare, ba tare da daukar kwararran matakan da za su samarwa da ‘yan Nijeriya sauki ba.

 

Ya zama wajibi, gwamnatin ta sani cewa, zabar ta aka yi kuma ba mulkin karfa-karfa ya dace ta rinka yiwa ‘yan kasar ba, musamman talakawa.

 

Malam Babbangida Yola; tabbas shekara 64 a cikin shekarun kasa ba abin wasa ba ne. Nijeriya ta fuskanci gwagwamarwa mai karfi a cikin wadannan shekarun. Tun daga yakin basasa da gano man fetur da bunkasar tattalin arziki a fannoni da dama. Dole a yaba da wadannan ci gaba, amma kuma in aka lura irin ci gaba da aka samu wasu kasashen da muka samu ‘yancin kai a daidai lokaci daya, sai muce abin bai kai yadda ake bukata ba. Matsalar a Nijeriya shi ne yadda shugabanin suna kasa tsayuwa su yi aiki yadda ya kamata da kuma yadda shugabannin bas a son ci gaba da ayyukan da wadanda sduka gaba suka fara na ci gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nazari Kan Gazawar Tsofaffin Ministocin Noma 52 Da Suka Shude A Nijeriya

Next Post

Gwamna Dauda Ya Kammala Biyan Bashin Ma’aikata Fiye Da Naira Biliyan 9

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

2 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

6 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

7 months ago
Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

7 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

8 months ago
Yanci
Ra'ayoyi

Matsalar Kifewar Kwale-kwale A Jihar Jigawa

9 months ago
Next Post
Gwamna Dauda Ya Kammala Biyan Bashin Ma’aikata Fiye Da Naira Biliyan 9

Gwamna Dauda Ya Kammala Biyan Bashin Ma'aikata Fiye Da Naira Biliyan 9

LABARAI MASU NASABA

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.