• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Shigowar Hunturu

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Rahotonni
0
Ra’ayoyinku A Kan Shigowar Hunturu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau mun kawo muku ra’ayoyin al’umma a kan hanyoyin fuskantar wannan lokaci na Hunturu, musamman yadda za a kare yara daga matsalolin da ke tattare da sanyin Hunturu da hanyoyin da ya kamata abi wajen ganin an kiyaye yawaitar tashin wuta (gobara) a irin wanna yanayi, ga dai ra’ayoyin maku.

Comr Isma’il Ibrahim Gusau

Wannan lokaci ne da ya kamata iyaye su kula da lafiyar’yan’yan su, domin basu kariya ga kamuwa da cutukan da sanyi ke haifar wa ga yaran su, kamar irinsu sanyin jiki da mura, da Sickler, Nemonear, da sauran su, a rinka sanya masu kayan sanyi, da hanasu wasa ruwa, a rinka yi masu wanka da ruwan zafi.

Fannin yawan goba, yakamata iyaye mata su kiyaye musamman masu amfani da Gas, saboda yawan gobarar da ke faruwa yanzu sakaci idan kaji musabbabin faruwar ta zaka ga sakaci ne ya haifar da ita, a kula da aiken yara kitchen, saboda gudun matsala, a rinka ajiye Gas wurin daya dace.

 Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Madallah da wannan maudu’i. Sannu da himma Hajiya Aunty Aysher Seyoji,  Gare ku iyaye musamman Mata da suke zaune tare da yaransu a gidaje a kowane lokaci. Yanayi na lokacin Hunturu yanayi ne mai wahalar sha’ani ga manya ma balle kananan yara. Idan aka ce an shiga yanayin na Hunturu to za ki ga tsafta ta yi karanci musamman idan aka ce miki ana bukatar a taba ruwane a lokacin tsaftacewar. Ba ma kamar ga kananan yara.

A wannan lokacin ne cututtuka suke shiga saboda ba’a kula da yanayin tsaftar yaran, wanda Babba ma za ki ga da yawa a cikin mutane sai sun dunduma ruwan zafi sannan za su iya yin wanka da shi saboda gujewa matsalar kamuwa da cuta musamman irin ta sanyi, to su kuma iyaye mata ba kowace ba ce take iya dunduma ruwan don yi wa yaranta wanka. Sannan kuma yawan amfani da ruwan sanyi a cikin yanayi na hunturu yana iya yi wa lafiya barazana da haifar da sauran cututtuka a cikin jiki.

Da fatan za mu kiyaye, don kulawa da lafiyarmu. Allah ya sa mu ga wucewa sa lafiya amin.

Faty Syaki

Wannan gaskiane, abinda zance game da yara .ke uwa ki kasance me tattalin yaranki ba kusaki yara sanyi safiya su hallara waje ko makotaba kamasu da safe ki musu wanka wannan wankan safen yana kore sanyi shafa musu mai a tafukan kafafunsa kisanya musu safa, ya zamakansu da hulunan sanyi ya rufe musu har kunnuwansu banda sa garwashi a daki wai don jin dumi wannan babban hatsari ne, wani lokaci gobaran ba zaka san ta inda ta tasoba sai dai nace Allah ya tsare dukacin al’umma baki daya. Allah ya sa mufita sanyin lafiya.

Abdul’aziz Mohammed

Tabbas haka ne, abu mafi muhimmanci da ya kamata iyaye su yi musamman ga yara shi ne su tabbatar daga karfe 5-6 an sanyawa yara kayan sanyi tare da da kauracewa yi wa yara wanka da ruwan sanyi.

Abdul’aziz Mohammed

A baiwa yara kula na musamman kamar kaurace wanka da ruwan sanyi. A tabbatar yayin da aka musu wanka an sanya tufafi da zai taimaka musu domin jin dumi_dumi a tare da su.

Nuruddeen Muhammad Funtua

A gaskiya ya kamata iyaye su kula sosai da sosai acikin wannan yanayi na sanyi musamman tsaftar yaran da tufafinsu wajen kwanciyar su da sauran abubuwa makamanci hakan sannan kuma mukula sosai da kashe abin girki musamman mu da muke karkara Allah ya karemu ya sa mufita lafiya

Sulaiman Muhammad

A daina aiken yara da sanyin Safiya, A sanyawa yara kaya masu nauyi, Kowa da kowa yana shan tea mai zafi sama sama, A daina aje Gas inda iska take kadawa in za a yi girki, A daina shiga da gawayi cikin daki da niyar jin dimi kuma ayi barci ba tare da an kashe shi ba, Masu skil cell a kula dasu sosai, Allah yasa muga karshensa lafiya

 Ra’ayi na musamman

Tashin Farashin Kayan-gona Yana Da Nasaba Da Chanjin Kuci.

Salam, Edita da masu karatu ina maku fatan alkairi, wato chijin kudi da gwamnati ke kokarin aiwatarwa tun yanzu talakan Nijeriya ya ga takansa abinci yana neman gagararmu wai kakar amfanin gona amma anawawar hatsi a kasuwa ina kuma tafiya ta yi nisa? Allah ka kawo mana agajinka ba don halinmu ba

Daga Umar-A-Umar Mazoji Matazu Katsina

07046493147


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hunturura'ayoyi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Taya Jonathan Murnar Cika Shekaru 65 

Next Post

2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk ‘Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

24 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

7 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

7 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk ‘Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku

2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk 'Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.