ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Shigowar Hunturu

by Aisha Seyoji
4 years ago
Hunturu

A yau mun kawo muku ra’ayoyin al’umma a kan hanyoyin fuskantar wannan lokaci na Hunturu, musamman yadda za a kare yara daga matsalolin da ke tattare da sanyin Hunturu da hanyoyin da ya kamata abi wajen ganin an kiyaye yawaitar tashin wuta (gobara) a irin wanna yanayi, ga dai ra’ayoyin maku.

Comr Isma’il Ibrahim Gusau

Wannan lokaci ne da ya kamata iyaye su kula da lafiyar’yan’yan su, domin basu kariya ga kamuwa da cutukan da sanyi ke haifar wa ga yaran su, kamar irinsu sanyin jiki da mura, da Sickler, Nemonear, da sauran su, a rinka sanya masu kayan sanyi, da hanasu wasa ruwa, a rinka yi masu wanka da ruwan zafi.

ADVERTISEMENT

Fannin yawan goba, yakamata iyaye mata su kiyaye musamman masu amfani da Gas, saboda yawan gobarar da ke faruwa yanzu sakaci idan kaji musabbabin faruwar ta zaka ga sakaci ne ya haifar da ita, a kula da aiken yara kitchen, saboda gudun matsala, a rinka ajiye Gas wurin daya dace.

 Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta

LABARAI MASU NASABA

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Madallah da wannan maudu’i. Sannu da himma Hajiya Aunty Aysher Seyoji,  Gare ku iyaye musamman Mata da suke zaune tare da yaransu a gidaje a kowane lokaci. Yanayi na lokacin Hunturu yanayi ne mai wahalar sha’ani ga manya ma balle kananan yara. Idan aka ce an shiga yanayin na Hunturu to za ki ga tsafta ta yi karanci musamman idan aka ce miki ana bukatar a taba ruwane a lokacin tsaftacewar. Ba ma kamar ga kananan yara.

A wannan lokacin ne cututtuka suke shiga saboda ba’a kula da yanayin tsaftar yaran, wanda Babba ma za ki ga da yawa a cikin mutane sai sun dunduma ruwan zafi sannan za su iya yin wanka da shi saboda gujewa matsalar kamuwa da cuta musamman irin ta sanyi, to su kuma iyaye mata ba kowace ba ce take iya dunduma ruwan don yi wa yaranta wanka. Sannan kuma yawan amfani da ruwan sanyi a cikin yanayi na hunturu yana iya yi wa lafiya barazana da haifar da sauran cututtuka a cikin jiki.

Da fatan za mu kiyaye, don kulawa da lafiyarmu. Allah ya sa mu ga wucewa sa lafiya amin.

Faty Syaki

Wannan gaskiane, abinda zance game da yara .ke uwa ki kasance me tattalin yaranki ba kusaki yara sanyi safiya su hallara waje ko makotaba kamasu da safe ki musu wanka wannan wankan safen yana kore sanyi shafa musu mai a tafukan kafafunsa kisanya musu safa, ya zamakansu da hulunan sanyi ya rufe musu har kunnuwansu banda sa garwashi a daki wai don jin dumi wannan babban hatsari ne, wani lokaci gobaran ba zaka san ta inda ta tasoba sai dai nace Allah ya tsare dukacin al’umma baki daya. Allah ya sa mufita sanyin lafiya.

Abdul’aziz Mohammed

Tabbas haka ne, abu mafi muhimmanci da ya kamata iyaye su yi musamman ga yara shi ne su tabbatar daga karfe 5-6 an sanyawa yara kayan sanyi tare da da kauracewa yi wa yara wanka da ruwan sanyi.

Abdul’aziz Mohammed

A baiwa yara kula na musamman kamar kaurace wanka da ruwan sanyi. A tabbatar yayin da aka musu wanka an sanya tufafi da zai taimaka musu domin jin dumi_dumi a tare da su.

Nuruddeen Muhammad Funtua

A gaskiya ya kamata iyaye su kula sosai da sosai acikin wannan yanayi na sanyi musamman tsaftar yaran da tufafinsu wajen kwanciyar su da sauran abubuwa makamanci hakan sannan kuma mukula sosai da kashe abin girki musamman mu da muke karkara Allah ya karemu ya sa mufita lafiya

Sulaiman Muhammad

A daina aiken yara da sanyin Safiya, A sanyawa yara kaya masu nauyi, Kowa da kowa yana shan tea mai zafi sama sama, A daina aje Gas inda iska take kadawa in za a yi girki, A daina shiga da gawayi cikin daki da niyar jin dimi kuma ayi barci ba tare da an kashe shi ba, Masu skil cell a kula dasu sosai, Allah yasa muga karshensa lafiya

 Ra’ayi na musamman

Tashin Farashin Kayan-gona Yana Da Nasaba Da Chanjin Kuci.

Salam, Edita da masu karatu ina maku fatan alkairi, wato chijin kudi da gwamnati ke kokarin aiwatarwa tun yanzu talakan Nijeriya ya ga takansa abinci yana neman gagararmu wai kakar amfanin gona amma anawawar hatsi a kasuwa ina kuma tafiya ta yi nisa? Allah ka kawo mana agajinka ba don halinmu ba

Daga Umar-A-Umar Mazoji Matazu Katsina

07046493147

Hunturu
Aisha Seyoji
+ postsBio
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Ra’ayoyinku A Kan Ba Da Bashi Ga Daliban Manyan Makarantu
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

MASU ALAKA

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
Rahotonni

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Next Post
2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk ‘Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku

2023: Tashoshin Jiragen Ruwa Da Na Kasa Da Matatun Mai Duk 'Yan Kasuwa Zan Ba —Atiku

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.