ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Tsadar Ragunan Layya A Wannan Shekarar (Ra’ayi)

by Aisha Seyoji
3 years ago
rago

Barkanmu da wannan lokaci barkanmu da sake saduwa a wannan fili mai albarka, Wannan makon mun ji ra’ayoyin kune a kan tsadar ragunan layya a wannan shekarar, shin menene ya kawo haka.

Kamal Y. Iyantama
Hauhawar tashin Dala, yayin da Naira ke kara faduwa a kullum, kuma an kasa bin hanyar saukaka hakan bare a yi tunanin gyarawa. Wannan hakki ya fi yawa a kan hukumomi zuwa wadanda abin ya shafa.
Allah ya kyauta !

  • Mene Ne Hukuncin Kebance Juma’a Da Azumi Idan Ta Dace Da Ranar Arfa?

Shamsi Umar Bakanike Dambatta
Ni dai anawa ganin ba komai bane ya kawo wannan tsada illa rashin kudi a hannun al’umma domin kuwa rashin kudi shi kesa ake ganin tsadar abu da fatan dai Allah (S.W.T) ya hurewa al’umma, don ni wallahi ko kaza ban siya ba gashi lokacin yana kara gabatowa.

ADVERTISEMENT

Aliyu Hassan Kumo
Akwai dalilai da dama wadanda suka sanya tsadar farashin, duba da yanayin kunci na rayuwa da kuma karancin kayan masarufi a sassa daban-daban.
Amma shi tsadar farashin Ragunan Layya yana da nasaba da yanayin da kasuwan take kai ne, akwai lokacin da za su iya sauka a lokaci daya, tunda dai da sauran lokaci kafin Sallah.

Kabiru Ado Muhd
Rashin tsaro da yawan hare-haren ta’addanci ke haifar da tsadar kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Sadeek Rufa’i Ɗanguguwa
To ni dai a iya nazarina abinda ya kawo tsadar Dabbobi a wannan Shekarar a Nijeriya shine:
SHANU: A bana Shanu sun yi tsada sosai sakamakon tsadar abinci, da matsin tattalin arkirin wannan kasa, wanda ya katse batun tafiya aikin Hajji ga duk wanda suka biya a bana wanda ya taimaka wajen kawo tsadar Dabbobi kwarai da gaske.
Abinda mutane basu fahimta ba shi ne su masu kiwo sukan fidda Dabbobi ne su sayar lokacin da suke bukatar samun kudaden domin biyan bukatar su. To dukkanin lokacin tafiya aikin Hajji masu kiwo daga Kamaru, Chadi da Nijeriya sukan fidda Shanu domin tafiya aikin Hajji wanda a kan samu Shanu da yawa sun cika kasuwa to wannan shekarar babu aikin zuwa Haji ga wanda ya biya wannan shekarar din, don haka babu bukatar fidda Shanu masu yawa a sayar shi ne yasa Shanun suka yi karanci sosai wannan ya haifar da tsadarsu.
Wannan karanci ya sanya Shanu sun ninka kudin su kusan Kashi 1½ wannan shi ne ainihin abinda ya janyo matsalar tsadar su a wannan lokaci. Wanda zaka ga wai har da Sa kwara daya 2.5M a bana.
RAGUNA: A bana suma sun yi karanci kwarai da gaske, kuma abincinsu ya yi tsada, mafi yawanci ana samar masu da abinci ne daga masu noman rani da na damuna daga abinda suka noma, to amman a wannan shekarar taki buhu daya ya kai dubu 30 kenan ya ninka kudinsa a shekarun baya sau uku. Wanda hakan tasa manoma da yawa suka kasa noma wa dabbobi abinda za su ci, don haka an samu karancin lura daga makiyaya, sakamakon kkarancin abincin, wannan tasa dole duk wanda ya lura da Ragonsa yadda ya kamata ya bukaci kudi masu auki, wanda hakan ke sawa mutane suke kallon kamar Dabbobin sun yi tsada ne.

Muhd Basheer Sa’ad
Tsadar kayan abinchi shi ya kawo hakan, tunda suma dabbobin abinci ake basu kuma abincin nan saya ake da kudi wannan shi ne dalili

Aisha Muazu
Maganar gaskiya komai ya yi tsada, dusa da duk wani abu da ya shafi kiwo ya yi tsada. Yakamata mu fahimci wannan tsadar rayuwar ba mu kadai ya shafa ba a kasar nan, Mafi akasari ko’ina a fadin kasar nan ana fama da tsadar rayuwa. Mu dai yi fatan Allah kawo mana sauki a al’amuranmu, Allah ya hore mana yadda zamu yi mu rufa wa kanmu asiri. Mai Hali ya sayi ragon layya kuma kar ya manta da makobta da yan’uwa, wanda bashi da dama ya yi hakuri, Allah saukaka mana da karfin ikonSa

Hibburrasul Na Sidi Gusau
Lallai wannan magana haka take, Allah ka bamu abinda zamu yi layya dashi

El Rufai
Kinsan ragunan da dollar ake Sayo su, kuma tayi tsada

Omar Naseer Imam
Toh bana kam ba’a cewa komai kawai dai Alhamdulillah

Nuruddeen Musa Indabawa
tsadar abincinsu da wahalar kiwonsu, sai kuma tsabar son kudin wasu da magunta da rashin tausayi, a gefe guda kuma ana fama da rashi albashi a wasu jihohin kamar Kano da sauransu
kasuwanni sunui jugum jugum

U-Darasip Sunusi
Zamanin da aka nufata hakan dai faru ne ya zo

Junaed Badamasi Abdul Khadir
Rashin samun shugabanci nagartacce da rashin kauna da kishin junanmu

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Hukunce-hukuncen Sallar Idi Da Layya (Fatawa)

Hukunce-hukuncen Sallar Idi Da Layya (Fatawa)

LABARAI MASU NASABA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.