• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Tsadar Ragunan Layya A Wannan Shekarar (Ra’ayi)

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Rahotonni
0
rago
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barkanmu da wannan lokaci barkanmu da sake saduwa a wannan fili mai albarka, Wannan makon mun ji ra’ayoyin kune a kan tsadar ragunan layya a wannan shekarar, shin menene ya kawo haka.

Kamal Y. Iyantama
Hauhawar tashin Dala, yayin da Naira ke kara faduwa a kullum, kuma an kasa bin hanyar saukaka hakan bare a yi tunanin gyarawa. Wannan hakki ya fi yawa a kan hukumomi zuwa wadanda abin ya shafa.
Allah ya kyauta !

  • Mene Ne Hukuncin Kebance Juma’a Da Azumi Idan Ta Dace Da Ranar Arfa?

Shamsi Umar Bakanike Dambatta
Ni dai anawa ganin ba komai bane ya kawo wannan tsada illa rashin kudi a hannun al’umma domin kuwa rashin kudi shi kesa ake ganin tsadar abu da fatan dai Allah (S.W.T) ya hurewa al’umma, don ni wallahi ko kaza ban siya ba gashi lokacin yana kara gabatowa.

Aliyu Hassan Kumo
Akwai dalilai da dama wadanda suka sanya tsadar farashin, duba da yanayin kunci na rayuwa da kuma karancin kayan masarufi a sassa daban-daban.
Amma shi tsadar farashin Ragunan Layya yana da nasaba da yanayin da kasuwan take kai ne, akwai lokacin da za su iya sauka a lokaci daya, tunda dai da sauran lokaci kafin Sallah.

Kabiru Ado Muhd
Rashin tsaro da yawan hare-haren ta’addanci ke haifar da tsadar kayayyaki

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Sadeek Rufa’i Ɗanguguwa
To ni dai a iya nazarina abinda ya kawo tsadar Dabbobi a wannan Shekarar a Nijeriya shine:
SHANU: A bana Shanu sun yi tsada sosai sakamakon tsadar abinci, da matsin tattalin arkirin wannan kasa, wanda ya katse batun tafiya aikin Hajji ga duk wanda suka biya a bana wanda ya taimaka wajen kawo tsadar Dabbobi kwarai da gaske.
Abinda mutane basu fahimta ba shi ne su masu kiwo sukan fidda Dabbobi ne su sayar lokacin da suke bukatar samun kudaden domin biyan bukatar su. To dukkanin lokacin tafiya aikin Hajji masu kiwo daga Kamaru, Chadi da Nijeriya sukan fidda Shanu domin tafiya aikin Hajji wanda a kan samu Shanu da yawa sun cika kasuwa to wannan shekarar babu aikin zuwa Haji ga wanda ya biya wannan shekarar din, don haka babu bukatar fidda Shanu masu yawa a sayar shi ne yasa Shanun suka yi karanci sosai wannan ya haifar da tsadarsu.
Wannan karanci ya sanya Shanu sun ninka kudin su kusan Kashi 1½ wannan shi ne ainihin abinda ya janyo matsalar tsadar su a wannan lokaci. Wanda zaka ga wai har da Sa kwara daya 2.5M a bana.
RAGUNA: A bana suma sun yi karanci kwarai da gaske, kuma abincinsu ya yi tsada, mafi yawanci ana samar masu da abinci ne daga masu noman rani da na damuna daga abinda suka noma, to amman a wannan shekarar taki buhu daya ya kai dubu 30 kenan ya ninka kudinsa a shekarun baya sau uku. Wanda hakan tasa manoma da yawa suka kasa noma wa dabbobi abinda za su ci, don haka an samu karancin lura daga makiyaya, sakamakon kkarancin abincin, wannan tasa dole duk wanda ya lura da Ragonsa yadda ya kamata ya bukaci kudi masu auki, wanda hakan ke sawa mutane suke kallon kamar Dabbobin sun yi tsada ne.

Muhd Basheer Sa’ad
Tsadar kayan abinchi shi ya kawo hakan, tunda suma dabbobin abinci ake basu kuma abincin nan saya ake da kudi wannan shi ne dalili

Aisha Muazu
Maganar gaskiya komai ya yi tsada, dusa da duk wani abu da ya shafi kiwo ya yi tsada. Yakamata mu fahimci wannan tsadar rayuwar ba mu kadai ya shafa ba a kasar nan, Mafi akasari ko’ina a fadin kasar nan ana fama da tsadar rayuwa. Mu dai yi fatan Allah kawo mana sauki a al’amuranmu, Allah ya hore mana yadda zamu yi mu rufa wa kanmu asiri. Mai Hali ya sayi ragon layya kuma kar ya manta da makobta da yan’uwa, wanda bashi da dama ya yi hakuri, Allah saukaka mana da karfin ikonSa

Hibburrasul Na Sidi Gusau
Lallai wannan magana haka take, Allah ka bamu abinda zamu yi layya dashi

El Rufai
Kinsan ragunan da dollar ake Sayo su, kuma tayi tsada

Omar Naseer Imam
Toh bana kam ba’a cewa komai kawai dai Alhamdulillah

Nuruddeen Musa Indabawa
tsadar abincinsu da wahalar kiwonsu, sai kuma tsabar son kudin wasu da magunta da rashin tausayi, a gefe guda kuma ana fama da rashi albashi a wasu jihohin kamar Kano da sauransu
kasuwanni sunui jugum jugum

U-Darasip Sunusi
Zamanin da aka nufata hakan dai faru ne ya zo

Junaed Badamasi Abdul Khadir
Rashin samun shugabanci nagartacce da rashin kauna da kishin junanmu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Sallah

Next Post

Hukunce-hukuncen Sallar Idi Da Layya (Fatawa)

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

4 days ago
layya
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

1 week ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

2 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

2 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

2 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

3 weeks ago
Next Post
Hukunce-hukuncen Sallar Idi Da Layya (Fatawa)

Hukunce-hukuncen Sallar Idi Da Layya (Fatawa)

LABARAI MASU NASABA

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

June 17, 2025
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

June 17, 2025
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

June 17, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

June 17, 2025
Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

June 17, 2025
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

June 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

June 17, 2025
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

June 17, 2025
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

June 17, 2025
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.