ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Hukuncin Kebance Juma’a Da Azumi Idan Ta Dace Da Ranar Arfa?

by Dakta Jamil Zarewa
4 years ago
Arfa

Mutane da yawa sun turo da tambayoyi suna son bayanin hukuncin kebance ranar Juma’a da Azumi idan ta dace da ranar Arfa. Akramakallah a yi mana bayani.

To Dan’uwa Annabi (SAW) ya kwadaitar game da yin Azumi ranar Arfa, inda ya tabbatar da cewa yana kankare zunubin shekaru biyu, Kamar yadda Tirmizi ya rawaito, sai dai ba a son wanda ya je Aikin Hajji ya yi azumin a ranar ARFA, ana so ya shagala da addu’a da zikiri a ranar.

  • Ya Halatta Mu Zubar Da Ciki Ni Da Mijina Idan Likita Ya Gaya Mana Yaron Da Za Mu Haifa Sikila Ne? (Fatawa)

Bukhari da Muslim sun rawaito hadisi daga Annabi (SAW) yana cewa: “Ka da dayanku ya azumci ranar Juma’a ita kadai, sai dai ya hada ta da ranar da take gabaninta ko ranar take kafin ita”.

ADVERTISEMENT

Bisa Hadisin da ya gabata za mu fahimci idan Arafa ta fado ranar Juma’a abin da yake daidai shi ne mutum ya azumci yinin da yake kafin ranar Arfa tare da ranar, saboda ba zai yiwu ya azumci yinin da yake bayan Arfa ba, tun da ya dace da ranar Sallah, Azumi kuma ranar Sallah ya haramta kamar yadda ya zo a Hadisin Umar Dan Khaddab.

Duk da cewa akwai malaman da suka halatta kebance ranar Juma’a da Azumi idan ta fado ranar Arfa saboda hujjar cewa an hana yin azumi ranar Juma’a ne ita kadai saboda kar a kebance ranar Juma’a da girmamawa.

LABARAI MASU NASABA

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

Wanda Kuma ya yi azumin Arfa ranar Juma’a, ya yi ne saboda Arfa ba saboda girmama Juma’a ba, sai dai azumin Arfa duk girman falalarsa azumi ne na Nafila, kuma Hadisin da ya hana kebance ranar Juma’a da azumi a kan azumin Nafila yake magana.

Duka kwanaki goman farkon Zulhijja kwanaki ne masu girman falala, babu kwanakin da suka fi su daraja a duniya, idan mutum ya azumci ranar takwas ya hada da ranar Arfa yana kan alkairi Maigirma da kabakin lada mai maiko, sannan zai fita daga sabanin malamai, kuma zai samar da nutsuwa a zuciyarsa.
Allah ne Mafi sani.

Yaya Hukuncin Kame Baki Ranar Idin Babbar Sallah?

Shin akwai wata madogara game da kame baki ranar idin babbar sallah ga wanda zai yi layya?
Wa alaikum assalam, Tabbas Tirmizy ya rawaito a hadisi mai lamba ta:542 cewa: “Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance ba ya cin wani abu ranar idin layya har sai ya dawo daga sallar idi.” Albani ya inganta shi. Sai dai hadisin bai bambance tsakanin wanda ya yi layya ba da wanda bai yi ba. Ban san wani daili ba ga wanda ya ce sai naman layya za a fara ci.
Allah ne mafi sani.

Arfa
Dakta Jamil Zarewa
+ postsBio
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Zan Iya Cin Bashin Banki Na Biya Aikin Hajji?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Mene Ne Hukuncin Koyon Ilimin Taurari A Shari’a?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 3, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Next Post
Tsuntsaye Jan-baki

Daminar Bana: Manoma Na Fargabar Bullar Tsuntsaye Jan-baki

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.