• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ma’aikata Ta Bana: Albashin Naira 615,000 Muke Bukata Don Mu Rayu – ‘Yan Kwadago

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Ranar Ma’aikata Ta Bana: Albashin Naira 615,000 Muke Bukata Don Mu Rayu – ‘Yan Kwadago
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da alama har yanzu tsugune ba ta kare ba duk da karin albashin da Gwamnatin Tarayya ta sanar da kashi 25 zuwa kashi 35 ga ma’aikatanta, ana jajebirin bikin ranar ma’aikata ta shekarar 2024, yayin da Shuga-ban Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC), Kwamared Joe Ajaero ya bayyana cewa karin da gwamati ta ce ta yi ba zai yi wani tasiri bai dan aka duba halin da kasar take ciki a yanzu.

Kwamared Ajero wanda ya yi bayanin haka a ranar Laraba a wani shirin gidan talabijin na Chan-nels, ya bayyana cewa, su babban abin da suke so shi ne gwamnati ta yi musu karin kudin da zai ishi ma’aikaci ya rayu a kasar nan ba kawai karin da zai ci gaba da tsunduma shi a cin bashi ba kullum.

  • Ranar Ma’aikata: Bayan Cike Giɓin Albashin Da Muka Gada, Za Mu Ci Gaba Da Inganta Walwalar Ma’aikata – Gwamnan Zamfara
  • Ranar Ma’aikata: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Laraba A Matsayin Hutu

“Mu abin da muke bukata shi ne albashin da za a iya biyan ma’aikaci yar ayu a Nijeriya. Kuma akalla shi ne a biya shi Naira 615,000. Kuma wannan ma a lissafin da muka yi ne kafin abubuwa su kara tsada irin na kwanan nan. Daga ciki a wata akalla ma’aikaci zai iya kashe Naira 110,000 a kan sufuri kawai, kudin wuta Naira 20,000 (wannan ma kafin a sanar da karin kudin wutar da aka yi kwanan baya ne). Sannan ma’aikacin da yake da akalla iyali mutum shida zai iya kashe Naira 50,000 a kiwon lafiya, shi ma idan babu tiyata ko wata lalaurar rashin lafiya da za ta ci kudi sosai. Haka nan kudin haya, ma’aikaci na bukatar biyan akalla Naira 40,000 duk wata, haka nan yana bukatar akalla Naira 20,000 na sayen fetur da kananzir a wata, ga batun abinci da kudin makaran-ta da kayan marmari da sauransu. Duka idan aka hada lissafi ya kamata a biya ma’aikaci Naira 615,000 don ya iya rayuwa a Nijeriya. Wanda bai amince da hakan ba kuma zai iya zuwa kasuwa da kansa ya yi safiyon kudaden abubuwan da muka ambata.” Ya bayyana.

Shugaban ‘yan kwadagon ya kuma yi nuni da cewa karin albashi don ya dace da yanayin da ake ciki a kasa abu ne da ake yi a duk fadin duniya, don haka bai kamata gwamnatin Nijeriya ta zama daban a cikin dangi ba, inda ya yi kira ga ma’aikata su kara jajircewa wajen cimma nasarar abubuwan da suka tasa a gaba na ganin an inganta walwalarsu.

A ranar Talata da dare ne dai, Gwamnatin Tarayya ta sanar da karin albashi da kashi 25 zuwa 35 ga ma’aikatanta wanda ta ce zai fara aiki tun daga ranar 1 ga Janairun 2024. Abin da ya rage dai yanzu shi ne lokacin da gwamnatin za ta biya bashin albashin da kuma dorewa da biyan karin, kasancewar har yanzu akwai masu bin bashin alawus na Naira 35,000 da ta ce za ta ba kowane ma’aikaci don rage radad-in cire tallafin maid aga watan Satumbar 2023.

Labarai Masu Nasaba

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hauhawar FarashiRanar Ma'aikataTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Damammakin Raya Kai Ga Matasan Kasashen Afirka

Next Post

Matsalolin Da Hukumar JAMB Ta Fuskanta A Jarrabawar Bana

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

31 minutes ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

1 hour ago
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

2 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

4 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

16 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

17 hours ago
Next Post
Jamb

Matsalolin Da Hukumar JAMB Ta Fuskanta A Jarrabawar Bana

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.