• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ma’aikata Ta Bana: Albashin Naira 615,000 Muke Bukata Don Mu Rayu – ‘Yan Kwadago

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Ranar Ma’aikata Ta Bana: Albashin Naira 615,000 Muke Bukata Don Mu Rayu – ‘Yan Kwadago
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da alama har yanzu tsugune ba ta kare ba duk da karin albashin da Gwamnatin Tarayya ta sanar da kashi 25 zuwa kashi 35 ga ma’aikatanta, ana jajebirin bikin ranar ma’aikata ta shekarar 2024, yayin da Shuga-ban Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC), Kwamared Joe Ajaero ya bayyana cewa karin da gwamati ta ce ta yi ba zai yi wani tasiri bai dan aka duba halin da kasar take ciki a yanzu.

Kwamared Ajero wanda ya yi bayanin haka a ranar Laraba a wani shirin gidan talabijin na Chan-nels, ya bayyana cewa, su babban abin da suke so shi ne gwamnati ta yi musu karin kudin da zai ishi ma’aikaci ya rayu a kasar nan ba kawai karin da zai ci gaba da tsunduma shi a cin bashi ba kullum.

  • Ranar Ma’aikata: Bayan Cike Giɓin Albashin Da Muka Gada, Za Mu Ci Gaba Da Inganta Walwalar Ma’aikata – Gwamnan Zamfara
  • Ranar Ma’aikata: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Laraba A Matsayin Hutu

“Mu abin da muke bukata shi ne albashin da za a iya biyan ma’aikaci yar ayu a Nijeriya. Kuma akalla shi ne a biya shi Naira 615,000. Kuma wannan ma a lissafin da muka yi ne kafin abubuwa su kara tsada irin na kwanan nan. Daga ciki a wata akalla ma’aikaci zai iya kashe Naira 110,000 a kan sufuri kawai, kudin wuta Naira 20,000 (wannan ma kafin a sanar da karin kudin wutar da aka yi kwanan baya ne). Sannan ma’aikacin da yake da akalla iyali mutum shida zai iya kashe Naira 50,000 a kiwon lafiya, shi ma idan babu tiyata ko wata lalaurar rashin lafiya da za ta ci kudi sosai. Haka nan kudin haya, ma’aikaci na bukatar biyan akalla Naira 40,000 duk wata, haka nan yana bukatar akalla Naira 20,000 na sayen fetur da kananzir a wata, ga batun abinci da kudin makaran-ta da kayan marmari da sauransu. Duka idan aka hada lissafi ya kamata a biya ma’aikaci Naira 615,000 don ya iya rayuwa a Nijeriya. Wanda bai amince da hakan ba kuma zai iya zuwa kasuwa da kansa ya yi safiyon kudaden abubuwan da muka ambata.” Ya bayyana.

Shugaban ‘yan kwadagon ya kuma yi nuni da cewa karin albashi don ya dace da yanayin da ake ciki a kasa abu ne da ake yi a duk fadin duniya, don haka bai kamata gwamnatin Nijeriya ta zama daban a cikin dangi ba, inda ya yi kira ga ma’aikata su kara jajircewa wajen cimma nasarar abubuwan da suka tasa a gaba na ganin an inganta walwalarsu.

A ranar Talata da dare ne dai, Gwamnatin Tarayya ta sanar da karin albashi da kashi 25 zuwa 35 ga ma’aikatanta wanda ta ce zai fara aiki tun daga ranar 1 ga Janairun 2024. Abin da ya rage dai yanzu shi ne lokacin da gwamnatin za ta biya bashin albashin da kuma dorewa da biyan karin, kasancewar har yanzu akwai masu bin bashin alawus na Naira 35,000 da ta ce za ta ba kowane ma’aikaci don rage radad-in cire tallafin maid aga watan Satumbar 2023.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hauhawar FarashiRanar Ma'aikataTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Damammakin Raya Kai Ga Matasan Kasashen Afirka

Next Post

Matsalolin Da Hukumar JAMB Ta Fuskanta A Jarrabawar Bana

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

8 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

8 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

9 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

9 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

12 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

13 hours ago
Next Post
Jamb

Matsalolin Da Hukumar JAMB Ta Fuskanta A Jarrabawar Bana

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.