• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ma’aikata Ta Bana: Albashin Naira 615,000 Muke Bukata Don Mu Rayu – ‘Yan Kwadago

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Ranar Ma’aikata Ta Bana: Albashin Naira 615,000 Muke Bukata Don Mu Rayu – ‘Yan Kwadago
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da alama har yanzu tsugune ba ta kare ba duk da karin albashin da Gwamnatin Tarayya ta sanar da kashi 25 zuwa kashi 35 ga ma’aikatanta, ana jajebirin bikin ranar ma’aikata ta shekarar 2024, yayin da Shuga-ban Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC), Kwamared Joe Ajaero ya bayyana cewa karin da gwamati ta ce ta yi ba zai yi wani tasiri bai dan aka duba halin da kasar take ciki a yanzu.

Kwamared Ajero wanda ya yi bayanin haka a ranar Laraba a wani shirin gidan talabijin na Chan-nels, ya bayyana cewa, su babban abin da suke so shi ne gwamnati ta yi musu karin kudin da zai ishi ma’aikaci ya rayu a kasar nan ba kawai karin da zai ci gaba da tsunduma shi a cin bashi ba kullum.

  • Ranar Ma’aikata: Bayan Cike Giɓin Albashin Da Muka Gada, Za Mu Ci Gaba Da Inganta Walwalar Ma’aikata – Gwamnan Zamfara
  • Ranar Ma’aikata: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Laraba A Matsayin Hutu

“Mu abin da muke bukata shi ne albashin da za a iya biyan ma’aikaci yar ayu a Nijeriya. Kuma akalla shi ne a biya shi Naira 615,000. Kuma wannan ma a lissafin da muka yi ne kafin abubuwa su kara tsada irin na kwanan nan. Daga ciki a wata akalla ma’aikaci zai iya kashe Naira 110,000 a kan sufuri kawai, kudin wuta Naira 20,000 (wannan ma kafin a sanar da karin kudin wutar da aka yi kwanan baya ne). Sannan ma’aikacin da yake da akalla iyali mutum shida zai iya kashe Naira 50,000 a kiwon lafiya, shi ma idan babu tiyata ko wata lalaurar rashin lafiya da za ta ci kudi sosai. Haka nan kudin haya, ma’aikaci na bukatar biyan akalla Naira 40,000 duk wata, haka nan yana bukatar akalla Naira 20,000 na sayen fetur da kananzir a wata, ga batun abinci da kudin makaran-ta da kayan marmari da sauransu. Duka idan aka hada lissafi ya kamata a biya ma’aikaci Naira 615,000 don ya iya rayuwa a Nijeriya. Wanda bai amince da hakan ba kuma zai iya zuwa kasuwa da kansa ya yi safiyon kudaden abubuwan da muka ambata.” Ya bayyana.

Shugaban ‘yan kwadagon ya kuma yi nuni da cewa karin albashi don ya dace da yanayin da ake ciki a kasa abu ne da ake yi a duk fadin duniya, don haka bai kamata gwamnatin Nijeriya ta zama daban a cikin dangi ba, inda ya yi kira ga ma’aikata su kara jajircewa wajen cimma nasarar abubuwan da suka tasa a gaba na ganin an inganta walwalarsu.

A ranar Talata da dare ne dai, Gwamnatin Tarayya ta sanar da karin albashi da kashi 25 zuwa 35 ga ma’aikatanta wanda ta ce zai fara aiki tun daga ranar 1 ga Janairun 2024. Abin da ya rage dai yanzu shi ne lokacin da gwamnatin za ta biya bashin albashin da kuma dorewa da biyan karin, kasancewar har yanzu akwai masu bin bashin alawus na Naira 35,000 da ta ce za ta ba kowane ma’aikaci don rage radad-in cire tallafin maid aga watan Satumbar 2023.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hauhawar FarashiRanar Ma'aikataTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Damammakin Raya Kai Ga Matasan Kasashen Afirka

Next Post

Matsalolin Da Hukumar JAMB Ta Fuskanta A Jarrabawar Bana

Related

Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

1 hour ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

4 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

5 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

8 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

10 hours ago
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

11 hours ago
Next Post
Jamb

Matsalolin Da Hukumar JAMB Ta Fuskanta A Jarrabawar Bana

LABARAI MASU NASABA

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.