• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

byCMG Hausa
3 years ago
Sin

Yau ranar 1 ga watan Oktoba, rana ce ta cika shekaru 73 da kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, wadda kuma ta yi daidai da ranar cika shekaru 62 da samun ‘yancin kan Nijeriya, ranar da ta alakanta kasashen biyu da ma al’ummunsu ta wata hanya ta musamman, duk da nisan da ke tsakaninsu. 

Tun bayan da kasashen biyu suka kulla huldar diplomasiyya a shekarar 1971, sun aiwatar da hadin gwiwa ta fannonin siyasa, da tattalin arziki, da al’adu, da kimiyya da dai sauransu, tare da cimma gaggaruman nasarori.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Inganta Hadin Gwiwa Da Sauran Kasashe A Bangaren Kimiyya Da Fasaha Da Kirkire-kirkire Da Kara Bude Kofa

A ranar 1 ga watan Yulin bana, jirgin ruwa na farko ya isa tashar ruwa ta Lekki da ke Lagos wadda ake ginawa, daga bisani, shugaban tarayyar Nijeriya Muhammadu Buhari ya fitar da sanarwa, inda ya bayyana murna, da farin ciki, game da yadda jirgin ya isa wannan tashar ruwa ta zamani irinta ta farko a Nijeriya, wadda kamfanin kasar Sin ke daukar nauyin ginawa.

Ya ce, tashar za ta samar da dimbin guraben aikin yi bayan da aka fara aiki da ita, baya ga kuma yadda za ta kyautata rayuwar al’ummar Nijeriya, tare da sa kaimin harkokin cinikayya a tsakanin Nijeriya da kasashen ketare, wanda hakan zai taimaka ga kyautata yanayin kasuwanci na kasar tare da janyo karin jarin waje.

A watan Agustan da ya gabata kuma, kasashen biyu sun cimma yarjejeniyar kafa tsarin hadin gwiwa a tsakanin asibitin jami’ar Peking ta kasar Sin, da ma asibitin jami’ar Abuja na Nijeriya, a wani kokari na inganta hadin gwiwar kasashen biyu ta fannin kiwon lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Sai kuma a watan Agusta, lokacin da aka kaddamar da mataki na biyu na aikin kafa fitilu masu amfani da hasken rana na ba da hannu ga motoci a birnin Abuja…

Dukkan wadannan wani bangare ne kawai na nasarorin da aka cimma a hadin gwiwar kasashen Sin da Nijeriya. Da tashar ruwa ta Lekki, da layin dogon Abuja-kaduna, da filin jiragen sama na Lagos, da tashar samar da wutar lantarki ta Zungeru, da kuma musayar kudade tsakanin kasashen biyu, da hadin gwiwar harba taurarin dan Adam da binciken teku, lallai hadin gwiwar kasashen biyu ya shafi fannonin tattalin arziki, da al’adu, da ba da ilmi, da kiwon lafiya, da hada-hadar kudi, da kimiyya da sauransu, wanda ya haifar da hakikanin alfanu ga al’ummar kasashen biyu.

Ranar 1 ga watan Oktoba, ta shaida yadda kasashen biyu suka yi gwagwarmayyar fita daga mawuyacin halin da suka samu kansu a ciki a baya, tare da bude sabon babinsu.

Muna da imanin cewa, bisa shawarar “ziri daya da hanya daya”, da ma tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, kasashen biyu za su karfafa dankon zumunci tsakaninsu, kuma hadin gwiwar kasashen biyu zai haifar da karin nasarori, da ma alfanu ga al’ummunsu. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version