• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau ranar 1 ga watan Oktoba, rana ce ta cika shekaru 73 da kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, wadda kuma ta yi daidai da ranar cika shekaru 62 da samun ‘yancin kan Nijeriya, ranar da ta alakanta kasashen biyu da ma al’ummunsu ta wata hanya ta musamman, duk da nisan da ke tsakaninsu. 

Tun bayan da kasashen biyu suka kulla huldar diplomasiyya a shekarar 1971, sun aiwatar da hadin gwiwa ta fannonin siyasa, da tattalin arziki, da al’adu, da kimiyya da dai sauransu, tare da cimma gaggaruman nasarori.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Inganta Hadin Gwiwa Da Sauran Kasashe A Bangaren Kimiyya Da Fasaha Da Kirkire-kirkire Da Kara Bude Kofa

A ranar 1 ga watan Yulin bana, jirgin ruwa na farko ya isa tashar ruwa ta Lekki da ke Lagos wadda ake ginawa, daga bisani, shugaban tarayyar Nijeriya Muhammadu Buhari ya fitar da sanarwa, inda ya bayyana murna, da farin ciki, game da yadda jirgin ya isa wannan tashar ruwa ta zamani irinta ta farko a Nijeriya, wadda kamfanin kasar Sin ke daukar nauyin ginawa.

Ya ce, tashar za ta samar da dimbin guraben aikin yi bayan da aka fara aiki da ita, baya ga kuma yadda za ta kyautata rayuwar al’ummar Nijeriya, tare da sa kaimin harkokin cinikayya a tsakanin Nijeriya da kasashen ketare, wanda hakan zai taimaka ga kyautata yanayin kasuwanci na kasar tare da janyo karin jarin waje.

A watan Agustan da ya gabata kuma, kasashen biyu sun cimma yarjejeniyar kafa tsarin hadin gwiwa a tsakanin asibitin jami’ar Peking ta kasar Sin, da ma asibitin jami’ar Abuja na Nijeriya, a wani kokari na inganta hadin gwiwar kasashen biyu ta fannin kiwon lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Sai kuma a watan Agusta, lokacin da aka kaddamar da mataki na biyu na aikin kafa fitilu masu amfani da hasken rana na ba da hannu ga motoci a birnin Abuja…

Dukkan wadannan wani bangare ne kawai na nasarorin da aka cimma a hadin gwiwar kasashen Sin da Nijeriya. Da tashar ruwa ta Lekki, da layin dogon Abuja-kaduna, da filin jiragen sama na Lagos, da tashar samar da wutar lantarki ta Zungeru, da kuma musayar kudade tsakanin kasashen biyu, da hadin gwiwar harba taurarin dan Adam da binciken teku, lallai hadin gwiwar kasashen biyu ya shafi fannonin tattalin arziki, da al’adu, da ba da ilmi, da kiwon lafiya, da hada-hadar kudi, da kimiyya da sauransu, wanda ya haifar da hakikanin alfanu ga al’ummar kasashen biyu.

Ranar 1 ga watan Oktoba, ta shaida yadda kasashen biyu suka yi gwagwarmayyar fita daga mawuyacin halin da suka samu kansu a ciki a baya, tare da bude sabon babinsu.

Muna da imanin cewa, bisa shawarar “ziri daya da hanya daya”, da ma tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, kasashen biyu za su karfafa dankon zumunci tsakaninsu, kuma hadin gwiwar kasashen biyu zai haifar da karin nasarori, da ma alfanu ga al’ummunsu. (Mai Zane: Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Ko INEC Za Ta Iya Gudanar Da Sahihin Zabe?

Next Post

Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

16 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

18 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

21 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

22 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

23 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.