ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Musamman Ga Sin Da Nijeriya

by CMG Hausa
4 years ago
Sin

Yau ranar 1 ga watan Oktoba, rana ce ta cika shekaru 73 da kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, wadda kuma ta yi daidai da ranar cika shekaru 62 da samun ‘yancin kan Nijeriya, ranar da ta alakanta kasashen biyu da ma al’ummunsu ta wata hanya ta musamman, duk da nisan da ke tsakaninsu. 

Tun bayan da kasashen biyu suka kulla huldar diplomasiyya a shekarar 1971, sun aiwatar da hadin gwiwa ta fannonin siyasa, da tattalin arziki, da al’adu, da kimiyya da dai sauransu, tare da cimma gaggaruman nasarori.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Inganta Hadin Gwiwa Da Sauran Kasashe A Bangaren Kimiyya Da Fasaha Da Kirkire-kirkire Da Kara Bude Kofa

A ranar 1 ga watan Yulin bana, jirgin ruwa na farko ya isa tashar ruwa ta Lekki da ke Lagos wadda ake ginawa, daga bisani, shugaban tarayyar Nijeriya Muhammadu Buhari ya fitar da sanarwa, inda ya bayyana murna, da farin ciki, game da yadda jirgin ya isa wannan tashar ruwa ta zamani irinta ta farko a Nijeriya, wadda kamfanin kasar Sin ke daukar nauyin ginawa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, tashar za ta samar da dimbin guraben aikin yi bayan da aka fara aiki da ita, baya ga kuma yadda za ta kyautata rayuwar al’ummar Nijeriya, tare da sa kaimin harkokin cinikayya a tsakanin Nijeriya da kasashen ketare, wanda hakan zai taimaka ga kyautata yanayin kasuwanci na kasar tare da janyo karin jarin waje.

A watan Agustan da ya gabata kuma, kasashen biyu sun cimma yarjejeniyar kafa tsarin hadin gwiwa a tsakanin asibitin jami’ar Peking ta kasar Sin, da ma asibitin jami’ar Abuja na Nijeriya, a wani kokari na inganta hadin gwiwar kasashen biyu ta fannin kiwon lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Sai kuma a watan Agusta, lokacin da aka kaddamar da mataki na biyu na aikin kafa fitilu masu amfani da hasken rana na ba da hannu ga motoci a birnin Abuja…

Dukkan wadannan wani bangare ne kawai na nasarorin da aka cimma a hadin gwiwar kasashen Sin da Nijeriya. Da tashar ruwa ta Lekki, da layin dogon Abuja-kaduna, da filin jiragen sama na Lagos, da tashar samar da wutar lantarki ta Zungeru, da kuma musayar kudade tsakanin kasashen biyu, da hadin gwiwar harba taurarin dan Adam da binciken teku, lallai hadin gwiwar kasashen biyu ya shafi fannonin tattalin arziki, da al’adu, da ba da ilmi, da kiwon lafiya, da hada-hadar kudi, da kimiyya da sauransu, wanda ya haifar da hakikanin alfanu ga al’ummar kasashen biyu.

Ranar 1 ga watan Oktoba, ta shaida yadda kasashen biyu suka yi gwagwarmayyar fita daga mawuyacin halin da suka samu kansu a ciki a baya, tare da bude sabon babinsu.

Muna da imanin cewa, bisa shawarar “ziri daya da hanya daya”, da ma tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, kasashen biyu za su karfafa dankon zumunci tsakaninsu, kuma hadin gwiwar kasashen biyu zai haifar da karin nasarori, da ma alfanu ga al’ummunsu. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

Sojoji Sun Kubutar Da Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Tagwayen Jarirai

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.