Sojojin Nijeriya biyu sun rasa ransu a wani iftila’in da ya afku a garin Aba na jihar Abia a yau Alhamis lokacin da ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka yi wa wasu sojojin kwanton ɓauna a mahadar Obikabia da ke tsaunin Ogbor.
Harin ya zo daidai da ranar tunawa da mayakan Biafra (IPOB) wanda yan asalin yankin Kudu maso Gabas ne, a yanzu haramtacciyar kungiyar ce a bisa dokar Nijeriya.
- Dattawan Kudancin Kano 103 Sun Buƙaci Gwamna Abba Ya Dawo Da Sarakuna 5 Da Aka Rushe
- Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara
Hotunan faifan bidiyo da aka saki a shafukan sada zumunta sun nuna sakamakon harin kwantan ɓaunar da aka yi, ciki har da wata motar soji da aka kona da kuma harbe-harbe a kan titunan da babu kowa, lamarin da ke nuni da zaman ɗarɗar a yayin da mazauna yankin suka bi dokar zaman gida ma tilas ba bisa ka’ida ba.
Har yanzu dai ba a san ko su waye maharan ba, kuma rundunar sojin Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba.
A baya dai kungiyar IPOB ta ayyana zaman gida a fadin jihohin Kudu maso Gabas domin karrama waɗanda aka kashe a yakin basasar Najeriya. Duk da cewa gwamnatin jihar Enugu ta yi watsi da wannan doka tare da kara ɗaukar matakan tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp