• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yanci: Jihar Kano Ta Zama Madubin Dubawa A Kan Kyakkyawan Shugabanci – Gwamna Abba

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Ranar ‘Yanci: Jihar Kano Ta Zama Madubin Dubawa A Kan Kyakkyawan Shugabanci – Gwamna Abba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano ta shirya taron kara wa juna sani a wani bangare na bukukuwan cikar Nijeriya shekara 64 da samun ‘yancin kai.

 

Taron wanda ya mayar da hankali kan irin ci gaban da aka samu da kalubalen da ke addabar kasar nan, ya gudana ne a dakin taro na fadar Gwamnatin Kano.

  • Kirkirar Kimiyya Da Fasaha Ta Kasar Sin Na Sa Kaimi Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Muhimman Abubuwa 10 Da Jawabin Tinubu Na Ranar ‘Yancin Kai Ya Kunsa 

Da yake jawabi a wurin taron, Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya tabo batutuwa masu motsa zuciya, inda ya bayyana cewa bisa sake fasalin shugabanci da tabbatar da rikon amana, Jihar Kano ta zama madubi ga jihohi da kuma fagen ci gaban siyasar kasar nan.

 

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Gwamna Abba bayan jinjina wa kokarin kwamitin da ya tsara wannan taro, wanda ya ce ya yi kyakkyanwan hange da tunanin zakulo masu gabatar da jawabai wadanda suka kasance mutane masu kima da daraja, ya yi karin haske kan kyakkyawan salon shugabancin gwamnatinsa.

 

Ya ce gwamnatin ta mayar da hankali sosai kan wasu muhimman ayyuka da suke da alaka da kyautata rayuwar al’ummar Jihar Kano kai-tsaye.

 

“Zan yi amfani da wannan dama domin bayyana wasu daga cikin manyan nasarorin da gwamnatin Kano ta samu a bangarori daban-daban, wannan kuma wani kokari ne na magance kalubalen da ya jima yana addabar rayuwar mazauna Kano.

 

“A bangaren ilimi, mun samu gagarumar nasarar sake farfado da sashin, hakan ya hada da ginawa tare da gyaran makarantu, daukar kwararrun malamai, samar da kayan koyo da koyarwa, haka kuma mun bujiro da tsarin ilmantarwa ta hanyar fasahar zamani da koyar da sana’o’i ga matasa.

 

“Sashin lafiya na cikin bangarorin da wannan gwamnati ke bai wa kulawa ta musamman, ta yadda aka daga darajar cibiyoyin kiwon lafiya, da kyautata tsarin kula da lafiyar mata masu ciki da kananan yara, kana an kuma yi duk mai yiwuwa wajen ganin ba a bar jama’ar karkara a baya ba. Sai kuma yadda muka tunkari kalubalen cututtuka kamar maleriya, karancin abinci mai gina jiki da sauran cututtukaka masu yaduwa.”

 

Har ila yau, Gwamna Abba ya nunar da cewa, sauran bangarorin da ke samun kyakkyawar kulawa a gwamnatinsa sun hada da sashin noma, tsaro, tallafa wa matasa da jari iri daban-daban, inganta tsarin aikin gwamnati da bayar da fifiko wajen biyan basussukan kudaden fansho da aka danne wa masu na tsawon lokaci.

 

Gwamnan ya kuma bayyana irin gagarumar nasarar da suka samu ta fuskar manyan ayyuka kamar kyautata muhalli, inganta harkar wasanni wadanda suka samar wa Jihar Kano gagarumin ci gaba.

 

Ya jaddada bukatar hadin kai a tsakanin al’ummar Jihar Kano domin kara samun nasarar da ake fata, yana mai cewar, “wannan kuma bai zai samu ba sai ta hanyar jajircewa, sadaukar da kai domin kare kimar al’ummarmu.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

Next Post

Kaso 40 Na ‘Yan Nijeriya Na Samun Wutar Lantarki Fiye Da Awa 20 A Kowace Rana — Minista

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

10 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

15 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

16 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

17 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

18 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

19 hours ago
Next Post
Kaso 40 Na ‘Yan Nijeriya Na Samun Wutar Lantarki Fiye Da Awa 20 A Kowace Rana — Minista

Kaso 40 Na 'Yan Nijeriya Na Samun Wutar Lantarki Fiye Da Awa 20 A Kowace Rana — Minista

LABARAI MASU NASABA

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.