• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida: AMDF Ta Nemi A Bai Wa ‘Yan Jarida Kariya A Afirka

by Sadiq
1 year ago
Jarida

Gidauniyar Ci Gaban Kafofin Watsa Labarai ta Afirka (AMDF), ta taya ‘yan jaridar Afirka murnar zagayowar ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya ta 2024.

Gidauniyar ta jaddada muhimmancin bai wa ‘yan jarida ‘yanci, mutuntawa da kuma riƙon amana.

  • WPFD 2024: Aikin Jarida A Yanayi Na Taɓarɓarewar Muhalli
  • ‘Gwamnatin Kano Da NNPP Sun Illata Siyasar Ganduje Duk Da Rashin Nasarar’

Wannan na cikin wata sanarwa da manajan kare ‘yancin ‘yan jarida na AMDF, Zhiroh Jatau, ya fitar a ranar Juma’a 3 ga watan Mayu, 2024.

AMDF ta nuna irin muhimmanci da rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen tabbatar da ‘yanci, da riƙon amana.

Taken ranar na bana, “Rawar Da ‘Yan Jarida Ke Takawa A Duniya: Yadda Aikin Jarida Ke Tunkarar Rikicin Muhalli,” ranar ta jaddada rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen bayar da shawarwarin samar da yanayi mai inganci.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Saboda haka gidauniyar ta jaddada muhimmancin fallasa kamfanoni da ƙungiyoyin da ke lalata albarkatun da ke doron ƙasa.

Wasu daga cikin matsalolin sun haɗa da sauyin yanayi, gurɓatar yanayi, da lalacewar hallitu, wanda gidauniyar ta bukaci ‘yan jarida su taka rawa wajen bayar da shawarwarin da za su kare muhalli daga gurɓacewa.

Gidauniyar ta ja hankali kan yiwuwar samun cin zarafin ‘yan jarida a ƙasashe irin su Ghana, Namibiya, Nijeriya, da Cape Verde, inda ake tsare ‘yan jarida, tare da kai wa kafafen watsa labarai samame sakamakon ayyukan da suke gudanarwa.

Abin takaici, yawancin ‘yan jaridar da ke bibiyar al’amuran da suka shafi cin hanci da rashawa a Afirka na fuskantar cin zarafi ta hanyar ɗauri da yi wa rayuwarsu barazana.

Saboda haka, AMDF ta yi kira ga hukumomin tsaro a Afrika da su ɗauki gaɓaren kare ‘yan jarida, tare da samar musu da yanayin da za su gudanar da ayyukansu cikin salama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe
Manyan Labarai

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja
Manyan Labarai

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Next Post
APC

Ba Mu Da Shirin Mayar Da Nijeriya Tsarin Jam’iyya Daya —APC

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.