• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yanci: Jihar Kano Ta Zama Madubin Dubawa A Kan Kyakkyawan Shugabanci – Gwamna Abba

by Abdullahi Muh'd Sheka
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Ranar ‘Yanci: Jihar Kano Ta Zama Madubin Dubawa A Kan Kyakkyawan Shugabanci – Gwamna Abba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano ta shirya taron ƙara wa juna sani a wani ɓangare na bukukuwan cikar ƙasar nan shekara 64 da samun ‘yancin kai.

Taron wanda ya mayar da hankali kan irin ci gaban da aka samu da ƙalubalen da ke addabar ƙasar nan, ya gudana ne a ɗakin taro na fadar Gwamnatin Kano (Coronation Hall).

Da yake jawabi, Gwamnan Jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya taɓo batutuwa masu motsa zuciya, inda ya bayyana cewa bisa sake fasalin shugabanci da tabbatar da riƙon amana, Jihar Kano ta zama madubi ga jihohi da kuma fagen ci gaban siyasar ƙasar nan.

  • NAPTIP Ta Kuɓutar Da Yara 19 Da Aka Sace A Kebbi 

Gwamna Abba Kabir Yusuf bayan jinjina wa ƙoƙarin kwamitin da ya tsara wannan taro wanda ya ce ya yi kyakkyanwan hange da tunanin zaƙulo masu gabatar da jawabai waɗanda suka kasance mutane masu kima da daraja, ya yi ƙarin haske kan kyakkyawan salon shugabancin gwamnatinsa.

Ya ce gwamnatin ta mayar da hankali sosai kan wasu muhimman ayyuka da suke da alaƙa da kyautata rayuwar al’ummar Jihar Kano kai-tsaye.
“Zan yi amfani da wannan dama domin bayyana wasu daga cikin manyan nasarorin da Gwamnatin Kano ta samu a ɓangarori daban-daban, wannan kuma wani ƙoƙari ne na magance ƙalubalen da ya jima yana addabar rayuwar mazauna Kano.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

‘A ɓangaren ilimi mun samu gagarumar nasarar sake farfaɗo da sashin, hakan ya haɗa da ginawa tare da gyaran makarantu, ɗaukar ƙwararrun malamai, samar da kayan koyo da koyarwa, haka kuma mun bujiro da tsarilimantarwa ta hanyar fasahar zamani da koyar da sana’o’i ga matasa.

“Sashin lafiya na cikin ɓangarorin da wannan gwamnati ke bai wa kulawa ta musamman, ta yadda aka ɗaga darajar cibiyoyin kiwon lafiya, da kyautata tsarin kula da lafiyar mata masu ciki da yara ƙanana, kana an kuma yi duk mai yiwuwa wajen ganin ba a bar jama’ar karkara a baya ba. Sai kuma yadda muka tunkari ƙalubalen cututtuka kamar maleriya, ƙarancin abinci mai gina jiki da sauran cututtukaka masu yaɗuwa.”

Har ila yau, Gwamna Abba Kabir ya nunar da cewa, sauran ɓangarorin da ke samun kyakkyawar kulawa a gwamnatinsa sun haɗa da sashin noma, Tsaro, Tallafa wa matasa da jari iri daban-daban, inganta tsarin aikin gwamnati da bayar da fifiko wajen biyan basussukan kuɗaɗen fansho da aka danne wa masu su tsawon lokaci.

Gwamnan ya kuma bayyana irin gagarumar nasarar da suka samu ta fuskar manyan ayyuka kamar kyautata muhalli, inganta harkar wasanni waɗanda suka samar wa Jihar Kano gagarumin ci gaba.

Daganan sai Gwamna Abba Kabir ya jaddada buƙatar haɗin kai a tsakanin al’ummar Jihar Kano domin ƙara samun nasarar da ake fata, yana mai cewar, “wannan kuma bai zai samu ba sai ta hanyar jajircewa, sadaukar da kai domin kare kimar al’ummar mu.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaGwamna Abba Gida-gidaGwamna Abba Kabirkano
ShareTweetSendShare
Previous Post

MƊD Ta Ƙaddamar Da Shirin “Muryoyi Daga Sahel” Karo Na Biyu

Next Post

‘Yancin Kai: PDP Ta Bukaci Tinubu Ya Rage Kudin Man Fetur

Related

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

13 hours ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

16 hours ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

22 hours ago
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

23 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

2 days ago
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Manyan Labarai

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

2 days ago
Next Post
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

‘Yancin Kai: PDP Ta Bukaci Tinubu Ya Rage Kudin Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.