Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Rashin Fitowar Mata Siyasa Abin Takaici Ne — Zariyatu

by Tayo Adelaja
September 24, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga El-Mansur Abubakar, Gombe

Rashin fitowar Mata a dama da su a siyasa musamman a jihar Gombe abun takaici ne domin har kullum ana barin mu a baya kuma mune rabin al’umma inji Hajiya Zariyatu Abubakar Hashidu.

samndaads

Hajiya Zariyatu Abubakar Hashidu, ita ce shugabar kungiyar nan da ba ta gwamnati ba ta Wildan Care Foundation, ita ta bayyana hakan a Gombe a lokacin da kungiyar ta ta kai ziyara tsangayar yan jarida dake fadar jihar Correspondent’s Chapel dan bayyana korafinsu akai.

Ta ce an bar Mata a baya Mazaje basa barin Matansu su fito a dama da su a siyasance bayan kuma sune suke da rinjaye a cikin al’umma sannan kuma ba’a kulawa da su wajen basu mukaman da suka kamata idan aka kafa gwamnati wanda hakan tasa suke so Mata su taso su tsaya da kafarsu dan ganin sun kwatowa kansu yanci.

“Ko tuki Mace take yi da ta wuce sai kaji an ce Mace ce to kaga ana dakushe ta kenan maimakon a karfafa mata guiwa”inji Zariyatu.

Shugabar ta Wildan Care Foundation, taci gaba da cewa a jihar Gombe da akwai Mata Yan Majalisa har guda biyu maimako duk lokacin da akayi zabe a samu kari sai aka wayi gari biyun ma babu yanzu cikin yan Majalisa sama da ashirin babu Mace ko daya.

“Ina kiran Mazaje da babbar Murya na ganin suna barin Matansu suna fitowa a dama da su a siyasa tunda suna barinsu suyi aikin gwamnati me yasa ba zasu basu dama su fito siyasa ba, kar su tauyewa yan uwan mu Mata yanci a duba fa’idar hakan a barsu su fito a fafata dasu ba gasa mu ke yi da Maza ba”Tace hakan.

Daga nan sai Hajiya Zariyatu tace idan ba’a samu karin yawaitar Mata a siyasa ba babu yadda za’ayi a samu kason da ake so na Mata masu rige da mukaman gwamnati ba’a jihar Gombe kadai ba a ko’ina a Najeriya.

Sannan sai ta yi amfani da wannan damar tayi kira ga hukumo da gwamnatoci har ma da Mazaje wajen bai wa Mata yancinsu na yin takara da kuma bari a zabesu ba tare da nuna musu wata tsana ko kushe ba.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Cancanta Ta Sa Mu Ka Nada Fati Kulani Jakadiyar Pantami – Hakimi

Next Post

Borno Ta Kashe Naira Biliyan 14 A Gina Hanyoyi 22 — Kwamishinan Ayyuka

RelatedPosts

Alaba

‘Yan Kasuwan Arewa A Legas Mu Hada Kai Don Cigaba – Muhammadu Alaba

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Hadin kai shi wani babban al’amari...

Jama'a

Taimaka Wa Jama’a Shi Ne Shugabanci Nagari -Matawalle Alagwadun Legas  

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai,   Matawallen Alagbado, Alhaji Muhammadu ya...

Samarun

Yadda Rasuwar Matashi Ta Jefa Mutane Cikin Alhini A Samarun Zariya

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Idris Umar, A ranar laraba ta wannan makon da...

Next Post

Borno Ta Kashe Naira Biliyan 14 A Gina Hanyoyi 22 — Kwamishinan Ayyuka

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version