• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Za Ta Fara Bai Wa Malamai Da Masu Unguwanni Alawus

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Za Ta Fara Bai Wa Malamai Da Masu Unguwanni Alawus
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Katsina ta ce za ta fara bai wa malaman Masallatan Juma’a da mataimakansu da masu unguwanni alawus-alawus domin karfafa musu gwiwa wajen yaki da rashin tsaro.

Gwamna Dikko Radda ne ya bayyana hakan bayan kaddamar da kwamitocin gudanarwa na kungiyar Katsina Community Watch Corps (KCSWC).

  • NFF Ta Sanar Da Ranar Fara Gasar ‘Federation Cup’ Ta Nijeriya
  • Gwamnan Zamfara Zai Binciki Badakalar Miliyan 774 A Hukumar Alhazai Ta Jihar

A wata sanarwa da babban sakataren yada labaransa, Ibrahim Kaula-Mohammed ya fitar, ya ruwaito Radda na cewa kwamitin zai hada kai da sauran jami’an tsaro wajen zakulo ‘yan bindiga a fadin jihar.

Ya ce mambobin kwamitin gudanarwa na kowace karamar hukuma 34 sun hada da kansila, hakimin gunduma, jami’in ‘yansanda na shiyya da wakilan hukumomin tsaro daban-daban.

Sannan ya ce akwai wakilai biyu na ‘yan kasuwa da kuma wakilan kungiyoyin addini.

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Gwamnan ya ce kwamitin zai sa ido tare da tantance ayyukan KCSWC a yankunansu tare da gabatar da rahoton wata-wata ga kwamishinan tsaron cikin gida na jihar.

Tun da fari, kwamishinan tsaron cikin gida na jihar, Dakta Nasiru Mu’azu-Danmusa, ya bayyana cewa sannu a hankali rashin tsaro na raguwa a fadin jihar tun da aka kafa KCSWC.

A nasu jawabin wakilan mai martaba Sarkin Katsina, Alhaji Aminu Nuhu Abdulkadir da mai shari’a Saddik Abdullahi Mahuta (mai ritaya), sun yaba wa gwamnan bisa daukar matakan magance matsalar rashin tsaro a jihar.

Abdulkadir, wanda shi ne hakimin Rimi da Abdullahi Mahuta, hakimin Malumfashi, sun yi alkawarin ci gaba da bai wa kwamitin goyon baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alawus-AlawusKatsinaKwamitiRaddaRashin Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Karbi ‘Yan Nijeriya 108 Da Suka Makale A Nijar

Next Post

Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Karawa Juna Sani Na Kasa Da Kasa Game Da Diflomasiyyar Kasar Sin

Related

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

3 hours ago
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

6 hours ago
Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

21 hours ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

23 hours ago
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

1 day ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

1 day ago
Next Post
Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Karawa Juna Sani Na Kasa Da Kasa Game Da Diflomasiyyar Kasar Sin

Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Karawa Juna Sani Na Kasa Da Kasa Game Da Diflomasiyyar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

July 31, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

2027: Ba Mu Kafa HaÉ—akarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

July 31, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

July 31, 2025
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

July 31, 2025
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

July 31, 2025
Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.