• English
  • Business News
Wednesday, June 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke rangadi a wata masana’anta mai aiki da fasahar zamani dake lardin Henan na kasar a jiya, ya ce yadda kasar Sin ta nace ga kokarin raya bangaren masana’antu, ya sauya kasar, daga wadda ke bukatar shigar da sabulu daga ketare, zuwa wadda ta mallaki dukkan nau’o’in masana’antu masu inganci. Ya ce, “Mun bi hanyar da ta dace.”

Hakika yanzu ko masu takara da Sin ma, sun yarda da ci gaban masana’antun kasar. Misali, Kyle Chan, mai nazarin manufofin Sin a jami’ar Princeton ta kasar Amurka, ya rubuta wani bayani, wanda jaridar New York Times ta wallafa a kwanan baya, inda ya ce kasar Sin tana kan gaba a duniya a dimbin fannonin masana’antu, kana yana sa ran ganin karfin masana’antun kasar ya kai kaso 45% na dukkan masana’antun duniya, zuwa shekarar 2030.

  • An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
  • ‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

Sai dai ta yaya kasar Sin ta cimma wannan nasara? A ganin mista Kyle, tsarin gwamnatin Sin na jagorantar aikin raya masana’antu ya taka muhimmiyar rawa, inda ya ba kasar Sin damar daidaita manufofi, da dora muhimmanci kan fannin masana’antu a kai a kai, ta yadda za ta iya cimma nasarar raya dimbin bangarori masu alaka da sabbin fasahohi na zamani.

Ganin nasarar da Sin ta samu ya sa mista Kyale damuwa sosai, a matsayinsa na Ba’amurke. Ya ce kasar Sin za ta iya zarce kasarsa ta Amurka, a karfin tattalin arziki da ingantattun fasahohi, ta yadda za ta iya daidaita tsare-tsare masu nasaba da iko a duniya.

Maganar Kyale ya shaida gaskiyar ra’ayin mista Stephen Akanbi, mai sharhi da na kan ga bayanansa a shafin yanar gizo na Opinion Nigeria. Ya taba bayyanawa cikin wani sharhinsa cewa, Amurka ta kan nuna kiyayya ga kasar Sin, ta fakewa da batutuwan “kiyaye tsaron kasa, da daidaiton ciniki, da hakkin dan Adam”. Amma a hakika, kasar tana tsoron kasar Sin, saboda nasarar da ta samu ta nuna wata sabuwar hanyar raya kasa, wadda za ta iya maye gurbin dabarar da kasashen yamma suka tsaya a kai.

Labarai Masu Nasaba

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

A ganin mista Akanbi, manufofin kasashen yamma ne dalilin da ya haifar da tafiyar hawainiyar tattalin arzikin Najeriya da na sauran kasashe dake nahiyar Afirka. Misali, kamfanonin kasashen yamma sun samu damar mamaye bangaren hakar ma’adinai na Najeriya, kana sun takaitawa kasar damar sarrafa ma’adinai, da ta raya masana’antu. Ban da haka, matsayin musamman na dalar Amurka a fannin ciniki, da yadda ake sarrafa farashin kudin, sun tsananta yanayin hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya, da jefa kamfanonin kasar cikin mawuyacin hali.

Ta yaya za a iya daidaita matsalolin da ake fuskanta? Mista Akanbi ya ba da shawarar daina dogaro da kasashen yamma, da tabbatar da bangarorin tattalin arzikin kasa da za a ba muhimmanci, bisa ra’ayin kasar, kamar yadda kasar Sin ta yi a baya. Ya ce, abokan hulda da Najeriya take bukata, su ne wadanda za su iya taimaka mata raya masana’antu, da zama mai zaman kai ta fuskar tattalin arziki. Saboda haka, karfafa hulda da kasashen BRICS, musamman ma kasar Sin, za su sanya Najeriya kama hanyar zama kasa mai karfin masana’antu, da na cinikayya.

Ci gaban kasa tamkar tafiyar da wani mutum yake yi. Idan wata hanyar da ake bi ba ta kai mutum inda ya nufa ba, to, sai a canza zuwa wata da daban. Wannan dabara ce da ta nuna hikima da sanin ya kamata. (Bello Wang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola

Next Post

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

Related

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Ra'ayi Riga

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

7 hours ago
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Ra'ayi Riga

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

1 day ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 days ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

6 days ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

1 week ago
Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Ra'ayi Riga

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

2 weeks ago
Next Post
Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki

Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki

June 11, 2025
haraji

Tinubu Ya Soke Yin Jawabi Ga ‘Yan Kasa Na Ranar Dimokuradiyya, Zai Yi Daga Zauren Majalisa

June 11, 2025
An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC

An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC

June 11, 2025
Dangote

Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4

June 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka

June 11, 2025
Kasuwancin Sin Da Afirka Ya Habaka Cikin Hanzari A Shekaru 25 Da Suka Gabata

Kasuwancin Sin Da Afirka Ya Habaka Cikin Hanzari A Shekaru 25 Da Suka Gabata

June 11, 2025
Filato

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato

June 11, 2025
He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa

He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa

June 11, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika

June 11, 2025
Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu

Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu

June 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.