• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke rangadi a wata masana’anta mai aiki da fasahar zamani dake lardin Henan na kasar a jiya, ya ce yadda kasar Sin ta nace ga kokarin raya bangaren masana’antu, ya sauya kasar, daga wadda ke bukatar shigar da sabulu daga ketare, zuwa wadda ta mallaki dukkan nau’o’in masana’antu masu inganci. Ya ce, “Mun bi hanyar da ta dace.”

Hakika yanzu ko masu takara da Sin ma, sun yarda da ci gaban masana’antun kasar. Misali, Kyle Chan, mai nazarin manufofin Sin a jami’ar Princeton ta kasar Amurka, ya rubuta wani bayani, wanda jaridar New York Times ta wallafa a kwanan baya, inda ya ce kasar Sin tana kan gaba a duniya a dimbin fannonin masana’antu, kana yana sa ran ganin karfin masana’antun kasar ya kai kaso 45% na dukkan masana’antun duniya, zuwa shekarar 2030.

  • An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
  • ‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

Sai dai ta yaya kasar Sin ta cimma wannan nasara? A ganin mista Kyle, tsarin gwamnatin Sin na jagorantar aikin raya masana’antu ya taka muhimmiyar rawa, inda ya ba kasar Sin damar daidaita manufofi, da dora muhimmanci kan fannin masana’antu a kai a kai, ta yadda za ta iya cimma nasarar raya dimbin bangarori masu alaka da sabbin fasahohi na zamani.

Ganin nasarar da Sin ta samu ya sa mista Kyale damuwa sosai, a matsayinsa na Ba’amurke. Ya ce kasar Sin za ta iya zarce kasarsa ta Amurka, a karfin tattalin arziki da ingantattun fasahohi, ta yadda za ta iya daidaita tsare-tsare masu nasaba da iko a duniya.

Maganar Kyale ya shaida gaskiyar ra’ayin mista Stephen Akanbi, mai sharhi da na kan ga bayanansa a shafin yanar gizo na Opinion Nigeria. Ya taba bayyanawa cikin wani sharhinsa cewa, Amurka ta kan nuna kiyayya ga kasar Sin, ta fakewa da batutuwan “kiyaye tsaron kasa, da daidaiton ciniki, da hakkin dan Adam”. Amma a hakika, kasar tana tsoron kasar Sin, saboda nasarar da ta samu ta nuna wata sabuwar hanyar raya kasa, wadda za ta iya maye gurbin dabarar da kasashen yamma suka tsaya a kai.

Labarai Masu Nasaba

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

A ganin mista Akanbi, manufofin kasashen yamma ne dalilin da ya haifar da tafiyar hawainiyar tattalin arzikin Najeriya da na sauran kasashe dake nahiyar Afirka. Misali, kamfanonin kasashen yamma sun samu damar mamaye bangaren hakar ma’adinai na Najeriya, kana sun takaitawa kasar damar sarrafa ma’adinai, da ta raya masana’antu. Ban da haka, matsayin musamman na dalar Amurka a fannin ciniki, da yadda ake sarrafa farashin kudin, sun tsananta yanayin hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya, da jefa kamfanonin kasar cikin mawuyacin hali.

Ta yaya za a iya daidaita matsalolin da ake fuskanta? Mista Akanbi ya ba da shawarar daina dogaro da kasashen yamma, da tabbatar da bangarorin tattalin arzikin kasa da za a ba muhimmanci, bisa ra’ayin kasar, kamar yadda kasar Sin ta yi a baya. Ya ce, abokan hulda da Najeriya take bukata, su ne wadanda za su iya taimaka mata raya masana’antu, da zama mai zaman kai ta fuskar tattalin arziki. Saboda haka, karfafa hulda da kasashen BRICS, musamman ma kasar Sin, za su sanya Najeriya kama hanyar zama kasa mai karfin masana’antu, da na cinikayya.

Ci gaban kasa tamkar tafiyar da wani mutum yake yi. Idan wata hanyar da ake bi ba ta kai mutum inda ya nufa ba, to, sai a canza zuwa wata da daban. Wannan dabara ce da ta nuna hikima da sanin ya kamata. (Bello Wang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola

Next Post

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

Related

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman
Ra'ayi Riga

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

7 days ago
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

2 weeks ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

2 weeks ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

2 weeks ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

3 weeks ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

3 weeks ago
Next Post
Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.