ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Da Tinubu Sun Fara Cacar Baki Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Atiku da Tinubu

Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu da takwararsa na jam’iyyar PDP, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar sun fara cacar baki kan zaben shekarar 2023.

Lokacin da PDP ta tsaya a kan bakanta na bayyana cewa Tinubu ya ci amanar jam’iyyarsa a 2007, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC ya bayyana cewa Atiku shi ne babban wanda ya ci amanar ‘yan Nijeriya wajen saba alkawan yarjejeniyar mulkin karba-karba tsakanin yankin arewaci da kuma kudancin Nijeriya.

  • Atiku Abubakar, Saraki, Tambuwal Da Bala Kaura Sun Taya Adeleke Murnar Lashe Zaɓen Osun

Cacar bakin dai ta fara kunno kai ne tun lokacin da Atiku ya zargi Tinubu na rashin goyon bayan jam’iyyar ACN a zaben shugaban kasa na 2007, saboda kin amincewa da akidarsa na yin takara tsakanin musulmi da musulmi.

ADVERTISEMENT

Atiku dai ya kasance shi ne dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar ACN a wancen lokaci, ya bayyana cewa Tinubu ya goyi bayan PDP a zaben 2007, bayan da shi Atiku ya tankwara a niyar tsohon gwamnan Jihar Legas na zama mataimakin shugaban kasa.

Dan takarar jam’iyyar PDP ya bayyana hakan ne lokacin wani shirin safe na gidan talabijin din Arise, inda ya ce takarar shugaban kasa tsakanin musulmi da musulmi ita ce babban matsalar da ta hada shi fada da Tinubu tun a 2007.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Tinubu shi ne ya kafa rushasshiyar jam’iyyar ACN jam kadan bayan da faduwar AD a cikin harkokin siyasa.

Yayin da Atiku ya kasance musulmi daga yankin arewa maso gabas, shi kuma Tinubu musulmi ne da ya fito daga yankin kudu maso yammacin Nijeriya.

A daidai lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Tinubu ya zabi Kashim Shettima, tsohon gwamnan Jihar Borno a matsayin abokin takararsa, wanda aka samu ce-ce-ku-ce daga wurin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da kin amincewa a wurin kungiyar kistoci sakamakon tikitin addini daya.

Da yake mayar da martani kan zabin da Tinubu na tsayar da musulmi abokin takararsa, Atiku ya ce sun dade suna kai ruwa-rana kan wannan matsalar da dan takarar shugaban kasa na APC, amma duk da haka su abokai ne.

Dan takarar shugaban kasa na PDP ya ce, “Babban matsalar da muka fara samu tsakanina da Tinubu a 2007 shi ne, batun tikitin takarar musulmi da musulmi.

A baya na fice daga ne saboda batun mulkin karba-karba, inda muka kafa ACN tare da Tinubu.

“Tinubu ya so ya kasance abokin takarana lokacin da aka ba ni takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar ACN a 2007, amma sai na ki yarda. Saboda haka ne ya goyi bayan Marigayi Umar Yaradua. Wannan shi ne farkon rabuwar kan da muka samu.

“Na dade ina kin amincewa da tikitin takarar musulmi da musulmi, domin kuwa akwai dimbin kabilu da addinai a Nijeriya, wanda ya kamata a samu daidaiton addinai a tsakaninmu.

Har yanzu mu abokanai ne, amma hakan bai hana mu samun rarrabuwar kai a cikin harkokin siyasa ba. Mun fara samun bambancin siyasa ne tun lokacin da muka kasance abokai.”
Da yake mayar da martani, mai magana da yawun dan takarar shugaban kasa na APC ya bayyana cewa akwai shaidu da ke nuna yadda Atiku ya dage wajen yaudarar ‘yan Nijeriya kan tikitin takarar shugaban kasa na musulmi da musulmi.

A cikin wata nasarwa da tsohon gwamnan Jihar Legas ya fitar a yammacin ranar Asabar wanda mai magana da yawunsa, Tunde Rahman ya rattaba hannu ya ce,
Atiku ya yi masa alkawarin mataimaki a 2007, amma daga baya ya kasa cika wannan alkawari kamar yadda a yanzu ya yi wa Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike.

A cewasa, tsohon mataimakin shugaban kasa ya kara yin amfani da irin yaudarar da ya saba na yi wa Wike alkawarin mataimakin shugaban kasa bayan gudanar da zaben fid da gwani na PDP amma ya kasa cikawa.

A game da sukar da tsohon mataimakin shugaban kasa yake yi na tikitin takarar shugaban kasa tsakanin musulmi da musulmi, Tinubu ya tunatar da Atiku cewa, ya yi yakin zama mataimakin Marigari Cif MKO Abiola a 1993, bayan da marigayin ya rasa samun tikitin takarar shugaban kasa.

Dan takarar APC ya ce ya kamata duk dan Nijeriya ya yi watsi da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, domin yana yunkurin kawo rarrabuwar kai wajen samun nasarar lashe zabe, wanda yake amfani da bambancin addini.

Shi ma daraktan watsa labarai na yakin neman zaben Tinubu, Bayo Onanuga ya mayar da martani kan tattaunawar da Atiku ya yi yana mai cewa, ya kadu lokacin da ya ji Atiku yana ta zuba karya.

Onanuga ya ce Atiku ya bayyana kansa a matsayin wanda ba zai iya gudanar da kyakkyawan shugabanci ba, sannan kuma ya kasance mutumin da ba za a iya amincewa da shi ba wajen danka masa ragamar shugabancin kasar nan.

Atiku da Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki

Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.