ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Da Tinubu Sun Fara Cacar Baki Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Atiku da Tinubu

Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu da takwararsa na jam’iyyar PDP, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar sun fara cacar baki kan zaben shekarar 2023.

Lokacin da PDP ta tsaya a kan bakanta na bayyana cewa Tinubu ya ci amanar jam’iyyarsa a 2007, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC ya bayyana cewa Atiku shi ne babban wanda ya ci amanar ‘yan Nijeriya wajen saba alkawan yarjejeniyar mulkin karba-karba tsakanin yankin arewaci da kuma kudancin Nijeriya.

  • Atiku Abubakar, Saraki, Tambuwal Da Bala Kaura Sun Taya Adeleke Murnar Lashe Zaɓen Osun

Cacar bakin dai ta fara kunno kai ne tun lokacin da Atiku ya zargi Tinubu na rashin goyon bayan jam’iyyar ACN a zaben shugaban kasa na 2007, saboda kin amincewa da akidarsa na yin takara tsakanin musulmi da musulmi.

ADVERTISEMENT

Atiku dai ya kasance shi ne dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar ACN a wancen lokaci, ya bayyana cewa Tinubu ya goyi bayan PDP a zaben 2007, bayan da shi Atiku ya tankwara a niyar tsohon gwamnan Jihar Legas na zama mataimakin shugaban kasa.

Dan takarar jam’iyyar PDP ya bayyana hakan ne lokacin wani shirin safe na gidan talabijin din Arise, inda ya ce takarar shugaban kasa tsakanin musulmi da musulmi ita ce babban matsalar da ta hada shi fada da Tinubu tun a 2007.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Tinubu shi ne ya kafa rushasshiyar jam’iyyar ACN jam kadan bayan da faduwar AD a cikin harkokin siyasa.

Yayin da Atiku ya kasance musulmi daga yankin arewa maso gabas, shi kuma Tinubu musulmi ne da ya fito daga yankin kudu maso yammacin Nijeriya.

A daidai lokacin da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Tinubu ya zabi Kashim Shettima, tsohon gwamnan Jihar Borno a matsayin abokin takararsa, wanda aka samu ce-ce-ku-ce daga wurin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da kin amincewa a wurin kungiyar kistoci sakamakon tikitin addini daya.

Da yake mayar da martani kan zabin da Tinubu na tsayar da musulmi abokin takararsa, Atiku ya ce sun dade suna kai ruwa-rana kan wannan matsalar da dan takarar shugaban kasa na APC, amma duk da haka su abokai ne.

Dan takarar shugaban kasa na PDP ya ce, “Babban matsalar da muka fara samu tsakanina da Tinubu a 2007 shi ne, batun tikitin takarar musulmi da musulmi.

A baya na fice daga ne saboda batun mulkin karba-karba, inda muka kafa ACN tare da Tinubu.

“Tinubu ya so ya kasance abokin takarana lokacin da aka ba ni takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar ACN a 2007, amma sai na ki yarda. Saboda haka ne ya goyi bayan Marigayi Umar Yaradua. Wannan shi ne farkon rabuwar kan da muka samu.

“Na dade ina kin amincewa da tikitin takarar musulmi da musulmi, domin kuwa akwai dimbin kabilu da addinai a Nijeriya, wanda ya kamata a samu daidaiton addinai a tsakaninmu.

Har yanzu mu abokanai ne, amma hakan bai hana mu samun rarrabuwar kai a cikin harkokin siyasa ba. Mun fara samun bambancin siyasa ne tun lokacin da muka kasance abokai.”
Da yake mayar da martani, mai magana da yawun dan takarar shugaban kasa na APC ya bayyana cewa akwai shaidu da ke nuna yadda Atiku ya dage wajen yaudarar ‘yan Nijeriya kan tikitin takarar shugaban kasa na musulmi da musulmi.

A cikin wata nasarwa da tsohon gwamnan Jihar Legas ya fitar a yammacin ranar Asabar wanda mai magana da yawunsa, Tunde Rahman ya rattaba hannu ya ce,
Atiku ya yi masa alkawarin mataimaki a 2007, amma daga baya ya kasa cika wannan alkawari kamar yadda a yanzu ya yi wa Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike.

A cewasa, tsohon mataimakin shugaban kasa ya kara yin amfani da irin yaudarar da ya saba na yi wa Wike alkawarin mataimakin shugaban kasa bayan gudanar da zaben fid da gwani na PDP amma ya kasa cikawa.

A game da sukar da tsohon mataimakin shugaban kasa yake yi na tikitin takarar shugaban kasa tsakanin musulmi da musulmi, Tinubu ya tunatar da Atiku cewa, ya yi yakin zama mataimakin Marigari Cif MKO Abiola a 1993, bayan da marigayin ya rasa samun tikitin takarar shugaban kasa.

Dan takarar APC ya ce ya kamata duk dan Nijeriya ya yi watsi da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, domin yana yunkurin kawo rarrabuwar kai wajen samun nasarar lashe zabe, wanda yake amfani da bambancin addini.

Shi ma daraktan watsa labarai na yakin neman zaben Tinubu, Bayo Onanuga ya mayar da martani kan tattaunawar da Atiku ya yi yana mai cewa, ya kadu lokacin da ya ji Atiku yana ta zuba karya.

Onanuga ya ce Atiku ya bayyana kansa a matsayin wanda ba zai iya gudanar da kyakkyawan shugabanci ba, sannan kuma ya kasance mutumin da ba za a iya amincewa da shi ba wajen danka masa ragamar shugabancin kasar nan.

Atiku da Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki

Ribar Dala Miliyan 240: ‘Yan Kasuwa Na Zargin CBN Da NNPC Da Take Musu Hakki

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.