• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ribar Noman Citta A Nijeriya

by Abubakar Abba
3 years ago
Noman citta

An dade ana noman citta a kasar nan, musaman Arewacin Nijeriya, ganin yadda noman ke samar wa manonanta kudi masu yawa.

A jihar Sakkwato da Zamfara da Jigawa da Kano da Katsina da Kudancin Kaduna, ana zuwa domin siyenta.

  • Yadda Ake Noman Zaitun A Zamanance

karamar hukumar Kaciya da Kagarko da Kubaca da ke cikin karamar hukumar Kagarko da Barde da Fori da ke karamar hukumar Jama’a, sai Kwoi da ke karamar hukumar Jaba, su ne manyan garuruwan da ke samar da kaso ma fi yawa na citta.
Wadannan yakunun, a daukacin fadin kasar nan inda nan ana zuwa siyenta, inda wasu kuma ke zuwa garin Kafancan domin siyenta.

Rahotannin sun bayyana cewa, a duk mako, tireloli 15 zuwa fiye da haka ke jigilarta daga Kafancan, inda a kowace jigila daya, ake dakon tan daga 26 zuwa 28.

Bugu da kari, nomanta da kasuwancinta da gyaranta na daga cikin harkoki ma fi girma da ke bunkasa harkokin arziki da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al’ummar Kudancin Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Cittar da ake noma wa a Kudancin Kaduna, wadda kuma aka yi amanna tana daga cikin ma fi kyau a duniya, a kan fara dibanta daga watan Nuwamba zuwa watan Afirilun.

A lokacin da ake ganiyar aikin cittar, mutane da yawa da suka hada da manya da kananan ’yan kasuwa da dillalai da direbobi da masu dako da masu gadi da masu aikin tsinta da shika da gyaran cittar, kowane kan kama aiki gadan-gadan, baya ga manomanta da ke fito wa da ita domin siyarwa a kasuwa.

Haka kuma, matasa na daga cikin wadanda ke cin gajiyar aikinta a karamar hukumar Jama’a da kuma garin Kaciya.
Sannan,haifaffun garuruwan, akwai masu aikin cittar da musamman suke baro garuruwansu su taho yankin don aikin gyaranta a kowace shekara.

Rahotannin sun ci gaba da cewa, lokacin da gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin a garkame iyakokin Nijerya, an ci gabna da jigilarta daga Nijeriya zuwa ketare kamar irin su, kasashen Benin da Ghana da Togo.

Sai dai, masu harkar cittar zuwa wannan yanki sun tabka asara a daidai lokacin da kasar ta rufe iyakokinta, inda hakan ya rutsa da tarin manyan motoci dauke da danyarta.

An ruwaito wata mata mai suna Jummai Jacob da ta dade tana sana’ar gyaranta a garin Kaciya ta bayyana cewa, ta fara aikin gyaranta ne a 2016.
Jummai ta ce ta fara gyaranta ne da buhu hudu a ranar farko amma a yanzu ina iya gyara buhu 30, inda ake biyanmu naira 100 a kan kowane buhu.

Jummai ta ce, da wannan aikin ne take daukar nauyin hidamar iyayenta da kula da karatun ’ya’yanta biyu.
Shi kuwa wani Sani Baba ya ce, ya kwashe fiye da shekara ashirin yana aikin cittar, inda ya kara da cewa, tun lokacin da ake biyansu naira 15 zuwa 20 a kowane buhu.

Ya kara da cewa, da aikin ne yake kula iyayensa da karatunsu, inda ya kara da cewa, aikin buhu 40 a kowace rana amma yanzu saboda leburori sun yi yawa ciki har da matan aure, hakan ya sa buhu 25 kawai take samu.

Shi ma wani mai aikin Malam Abdullahi, ya ce ya shafe shekara hudu yana sana’ar siyan da buhunan citta bayan an tsince manya da kanana an tankade ta, sai a saya domin sayar wa ’yankoli.
Ya ce da wannan aikin yake daukar nauyin karatun ’ya’yansa da kuma yin dawainiyar gidansa.

Shi kuma wani matashi da yake yin aikin Sani Musa ya bayyana cewa, da kudin da yake samu na aikin gyranta ne yake taimaka wa kansa da kuma iyayensa, inda ya ci gaba da cewa, ya fara zuwa aikin ne tun ina dan shekara 11, inda yake samun daga naira 200 zuwa naira 500.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Next Post
Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Gaggauta Daidaitawa Da Ma Dage Takunkuman Da Aka Kakabawa Kasashen Afirka Da Ba Su Biya Bukatun Halin Da Ake Ciki Ba

Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Gaggauta Daidaitawa Da Ma Dage Takunkuman Da Aka Kakabawa Kasashen Afirka Da Ba Su Biya Bukatun Halin Da Ake Ciki Ba

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.